Home Taska Samar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46

Samar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46

Soji

Samar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46

 

Sojojin Najeriya sun sanar da kama ƴan ƙasashen waje 46 a wani aikin samar da tsaro da suka gudanar a jihar Ogun da ke yankin kudu maso yammacin ƙasar.

A cewar rundunar, an kai samamen ne a ranar Alhamis a yankunan Ijebu Imushin da Ijebu Ilese tare da wasu ƙauyuka da ke kusa, bayan samun bayanan sirri masu muhimmanci.

Mai magana da yawun rundunar, Idereghi Samuel Akari, ya ce binciken farko ya nuna cewa mutanen sun shafe kusan watanni shida a Najeriya ba tare da takardun izinin zama ba.

Ya ƙara da cewa mutanen sun shaida wa jami’an bincike cewa su ‘yan kasuwa ne da ma’aikata masu alaƙa da kamfanin QNET, wani kamfanin sayar da kayayyaki ta intanet mai hedikwata a Hong Kong.

Sai dai kamfanin QNET ya sha fuskantar zarge-zarge a Najeriya, inda hukumomi ke danganta kamfanin da damfara da safarar mutane da kuma shigo da mutane ba bisa ƙa’ida ba amma kuma kamfanin ya musanta hannu a irin waɗannan ayyuka, yana mai cewa yana nesanta kansa da masu amfani da sunansa wajen aikata laifi.

Kamen na zuwa ne a daidai lokacin da ake ƙara nuna damuwa a yammacin Afirka kan wasu ƙungiyoyin da ake zargi da amfani da sunan kamfanin wajen yaudarar mutane da alƙawuran samun aiki a ƙasashen waje da kuma samun kuɗi cikin sauƙi.

Daga cikin mutanen da aka kama, guda 18 ‘yan ƙasar Burkina Faso ne, 23 kuma daga Ivory Coast, huɗu daga Togo yayin da kuma mutum ɗaya daga Senegal ne.

Daga bisani, an miƙa waɗanda aka kama ga Hukumar Shige da Fice ta Najeriya domin ci gaba da bincike.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Matatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga Legas
X whatsapp