Home Taska Samar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46

Samar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46

Soji

Samar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46

 

Sojojin Najeriya sun sanar da kama ƴan ƙasashen waje 46 a wani aikin samar da tsaro da suka gudanar a jihar Ogun da ke yankin kudu maso yammacin ƙasar.

A cewar rundunar, an kai samamen ne a ranar Alhamis a yankunan Ijebu Imushin da Ijebu Ilese tare da wasu ƙauyuka da ke kusa, bayan samun bayanan sirri masu muhimmanci.

Mai magana da yawun rundunar, Idereghi Samuel Akari, ya ce binciken farko ya nuna cewa mutanen sun shafe kusan watanni shida a Najeriya ba tare da takardun izinin zama ba.

Ya ƙara da cewa mutanen sun shaida wa jami’an bincike cewa su ‘yan kasuwa ne da ma’aikata masu alaƙa da kamfanin QNET, wani kamfanin sayar da kayayyaki ta intanet mai hedikwata a Hong Kong.

Sai dai kamfanin QNET ya sha fuskantar zarge-zarge a Najeriya, inda hukumomi ke danganta kamfanin da damfara da safarar mutane da kuma shigo da mutane ba bisa ƙa’ida ba amma kuma kamfanin ya musanta hannu a irin waɗannan ayyuka, yana mai cewa yana nesanta kansa da masu amfani da sunansa wajen aikata laifi.

Kamen na zuwa ne a daidai lokacin da ake ƙara nuna damuwa a yammacin Afirka kan wasu ƙungiyoyin da ake zargi da amfani da sunan kamfanin wajen yaudarar mutane da alƙawuran samun aiki a ƙasashen waje da kuma samun kuɗi cikin sauƙi.

Daga cikin mutanen da aka kama, guda 18 ‘yan ƙasar Burkina Faso ne, 23 kuma daga Ivory Coast, huɗu daga Togo yayin da kuma mutum ɗaya daga Senegal ne.

Daga bisani, an miƙa waɗanda aka kama ga Hukumar Shige da Fice ta Najeriya domin ci gaba da bincike.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Samar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46Ta'addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da ke AbujaAn Ceto Matar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaHauhawar Farashin Kayan Masarufi a Najeriya ya ƙaru Zuwa Kashi 15.93Rundunar Sojin Najeriya ta Gudanar da Hare-Hare Kan Maɓoyar ƴan Bindiga a Jihar KatsinaZaben 2027: NDC ta Tsayar da Ɗan Kwankwaso Mataimakin ɗan Takarar Gwamnan KanoKotu ta Umarci INEC da ta Soke Rajistar ADC Tare da Jam’iyyu 4Manyan Tsofaffin Jami'an Soji 10 da Suka Rasa Rayukansu a Hannun ƴan Ta'addaTarihin Rayuwar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaMatsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar AbujaDuk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da 'Yan Ta'adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda - Christopher MusaFarashin ɗanyen Mai ya Faɗi Bayan Amurka ta Soke Sabbin Hare-Haren kaiwa IranAmurka ta yi sulhu kan yaƙin da ta ke yi da Iran - TrumpMajalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan JihaHukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar Neja
X whatsapp