Home Taska ‘Yan Bindiga sun ƙone shingen Jami’an NSCDC Tare da Garkuwa da Mutum...

‘Yan Bindiga sun ƙone shingen Jami’an NSCDC Tare da Garkuwa da Mutum 1 a Jihar Kebbi

‘Yan Bindiga sun ƙone shingen Jami’an NSCDC Tare da Garkuwa da Mutum 1 a Jihar Kebbi

Wasu ’yan bindiga sun kai hari garin Tsamiya da ke Ƙaramar Hukumar Bagudo a Jihar Kebbi, inda suka ƙone shingen bincike na rundunar Sibil Difens (NSCDC), tare da lalata wasu gine-gine a yankin.

Rahotanni sun ce ’yan bindigar sun kuma yi garkuwa da wani mutum mai suna Alhaji Yusuf Bazamfare yayin harin da suka kai a ranar Asabar.

A cewar mazauna yankin, ’yan bindigar sun kuma ƙone gidan karuwai da kuma gidan wani mutum mai suna Sule Mai Goge sannan suka tsere.

Mai magana da yawun Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kebbi, SP Bashir Usman, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce rundunar ta tura jami’anta zuwa yankin nan take bayan samun rahoton harin.

Ya ce Kwamishinan ’yan sandan jihar ya bayar da umarnin tura ƙarin jami’an tsaro domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma a yankin.

“An fara bincike kan lamarin, sannan ana ƙoƙarin gano inda aka kai wanda aka yi garkuwa da shi domin kuɓutar da shi,” in ji shi.

SP Bashir Usman ya kuma buƙaci mazauna yankin da su kwantar da hankali tare da bai wa jami’an tsaro haɗin kai da sahihan bayanai da za su taimaka wajen gudanar da aikin ceto da bincike.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Meyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu MohammedJami'an Tsaro Sun Kai Farmaki Sansanin IPOB/ESN, Sun Kawar da 'Yan Ta'adda 6 a AnambraOperation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Lalata Motocin Yaƙi Guda Biyu na ISWAP, Sannan Ya Kawar da Ƴan Ta'adda da Dama a BornoMai fafutuka Mahdi Shehu ya yi Gargadin Cewa Kudirin Dokar NGO Zai iya Shafar Masallatai, Coci, da Ƙungiyoyin ɗalibaiRikicin Karkashin Mulkin APC a Katsina: ADC na Radda da CSO Har Yanzu Suna Tsare a Hannun Masu ba Tinubu Shawara, MasariAnambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron Hanya
X whatsapp