‘Yan Bindiga sun ƙone shingen Jami’an NSCDC Tare da Garkuwa da Mutum 1 a Jihar Kebbi
Wasu ’yan bindiga sun kai hari garin Tsamiya da ke Ƙaramar Hukumar Bagudo a Jihar Kebbi, inda suka ƙone shingen bincike na rundunar Sibil Difens (NSCDC), tare da lalata wasu gine-gine a yankin.
Rahotanni sun ce ’yan bindigar sun kuma yi garkuwa da wani mutum mai suna Alhaji Yusuf Bazamfare yayin harin da suka kai a ranar Asabar.
A cewar mazauna yankin, ’yan bindigar sun kuma ƙone gidan karuwai da kuma gidan wani mutum mai suna Sule Mai Goge sannan suka tsere.
Read Also:
Mai magana da yawun Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kebbi, SP Bashir Usman, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce rundunar ta tura jami’anta zuwa yankin nan take bayan samun rahoton harin.
Ya ce Kwamishinan ’yan sandan jihar ya bayar da umarnin tura ƙarin jami’an tsaro domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma a yankin.
“An fara bincike kan lamarin, sannan ana ƙoƙarin gano inda aka kai wanda aka yi garkuwa da shi domin kuɓutar da shi,” in ji shi.
SP Bashir Usman ya kuma buƙaci mazauna yankin da su kwantar da hankali tare da bai wa jami’an tsaro haɗin kai da sahihan bayanai da za su taimaka wajen gudanar da aikin ceto da bincike.











