Home Taska ‘Yan Bindiga sun ƙone shingen Jami’an NSCDC Tare da Garkuwa da Mutum...

‘Yan Bindiga sun ƙone shingen Jami’an NSCDC Tare da Garkuwa da Mutum 1 a Jihar Kebbi

‘Yan Bindiga sun ƙone shingen Jami’an NSCDC Tare da Garkuwa da Mutum 1 a Jihar Kebbi

Wasu ’yan bindiga sun kai hari garin Tsamiya da ke Ƙaramar Hukumar Bagudo a Jihar Kebbi, inda suka ƙone shingen bincike na rundunar Sibil Difens (NSCDC), tare da lalata wasu gine-gine a yankin.

Rahotanni sun ce ’yan bindigar sun kuma yi garkuwa da wani mutum mai suna Alhaji Yusuf Bazamfare yayin harin da suka kai a ranar Asabar.

A cewar mazauna yankin, ’yan bindigar sun kuma ƙone gidan karuwai da kuma gidan wani mutum mai suna Sule Mai Goge sannan suka tsere.

Mai magana da yawun Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kebbi, SP Bashir Usman, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce rundunar ta tura jami’anta zuwa yankin nan take bayan samun rahoton harin.

Ya ce Kwamishinan ’yan sandan jihar ya bayar da umarnin tura ƙarin jami’an tsaro domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma a yankin.

“An fara bincike kan lamarin, sannan ana ƙoƙarin gano inda aka kai wanda aka yi garkuwa da shi domin kuɓutar da shi,” in ji shi.

SP Bashir Usman ya kuma buƙaci mazauna yankin da su kwantar da hankali tare da bai wa jami’an tsaro haɗin kai da sahihan bayanai da za su taimaka wajen gudanar da aikin ceto da bincike.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Matatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga Legas
X whatsapp