Home Taska Rundunar Sojin Najeriya ta Gudanar da Hare-Hare Kan Maɓoyar ƴan Bindiga a...

Rundunar Sojin Najeriya ta Gudanar da Hare-Hare Kan Maɓoyar ƴan Bindiga a Jihar Katsina

Rundunar Soji

Rundunar Sojin Najeriya ta Gudanar da Hare-Hare Kan Maɓoyar ƴan Bindiga a Jihar Katsina

 

Rundunar Sojin Najeriya ta ce ta ƙaddamar da wasu zafafan hare-hare kan ƴan bindiga a wasu yankuna na jihar Katsina da ke arewa maso gabashin ƙasar.

Wannan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan mutuwar tsohon Janar na soja a hannun ƴan bindiga.

A wata sanarwa da jami’in yada labarai na rundunar, Laftanar Kanal Aliyu Danja, ya fitar ranar Litinin, ya bayyana cewa an fara wannan farmakin mai taken ‘Operation Clean Sweep III’ domin fatattakar ƴan bindiga a ƙaramar hukumar Matazu da wasu yankunan Katsina.

Ya ce sun fara wannan farmaki ne tun ranar 14 ga watan Yunin 2026.

Rundunar ta ƙaddamar da hare-haren ne ƙarƙashin Operation Fansan Yamma da ke aiki a yankin Arewa maso yammacin ƙasar.

Sanarwar ta ce an samu nasarori musamman a yankunan tsaunukan Dikkawa da sauran ƙauyukan da ke kusa.

Ta ce ta kai samamen ne a yankunan Adua, Nasarawa da Karaduwa, inda ya kai ga gano da lalata maboyar ‘yan ta’adda, wuraren ajiye kayayyaki da sauran cibiyoyin da suke amfani da su.

“A lokacin harin, an lalata maɓoyar ƴan ta’adda da kayayyakinsu da motocinsu, kuma hakan ya rage musu ƙarfin kai hari a yankin,” in ji sanarwar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Samar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46Ta'addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da ke AbujaAn Ceto Matar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaHauhawar Farashin Kayan Masarufi a Najeriya ya ƙaru Zuwa Kashi 15.93Rundunar Sojin Najeriya ta Gudanar da Hare-Hare Kan Maɓoyar ƴan Bindiga a Jihar KatsinaZaben 2027: NDC ta Tsayar da Ɗan Kwankwaso Mataimakin ɗan Takarar Gwamnan KanoKotu ta Umarci INEC da ta Soke Rajistar ADC Tare da Jam’iyyu 4Manyan Tsofaffin Jami'an Soji 10 da Suka Rasa Rayukansu a Hannun ƴan Ta'addaTarihin Rayuwar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaMatsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar AbujaDuk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da 'Yan Ta'adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda - Christopher MusaFarashin ɗanyen Mai ya Faɗi Bayan Amurka ta Soke Sabbin Hare-Haren kaiwa IranAmurka ta yi sulhu kan yaƙin da ta ke yi da Iran - TrumpMajalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan JihaHukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar Neja
X whatsapp