Rundunar Sojin Najeriya ta Gudanar da Hare-Hare Kan Maɓoyar ƴan Bindiga a Jihar Katsina
Rundunar Sojin Najeriya ta ce ta ƙaddamar da wasu zafafan hare-hare kan ƴan bindiga a wasu yankuna na jihar Katsina da ke arewa maso gabashin ƙasar.
Wannan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan mutuwar tsohon Janar na soja a hannun ƴan bindiga.
A wata sanarwa da jami’in yada labarai na rundunar, Laftanar Kanal Aliyu Danja, ya fitar ranar Litinin, ya bayyana cewa an fara wannan farmakin mai taken ‘Operation Clean Sweep III’ domin fatattakar ƴan bindiga a ƙaramar hukumar Matazu da wasu yankunan Katsina.
Read Also:
Ya ce sun fara wannan farmaki ne tun ranar 14 ga watan Yunin 2026.
Rundunar ta ƙaddamar da hare-haren ne ƙarƙashin Operation Fansan Yamma da ke aiki a yankin Arewa maso yammacin ƙasar.
Sanarwar ta ce an samu nasarori musamman a yankunan tsaunukan Dikkawa da sauran ƙauyukan da ke kusa.
Ta ce ta kai samamen ne a yankunan Adua, Nasarawa da Karaduwa, inda ya kai ga gano da lalata maboyar ‘yan ta’adda, wuraren ajiye kayayyaki da sauran cibiyoyin da suke amfani da su.
“A lokacin harin, an lalata maɓoyar ƴan ta’adda da kayayyakinsu da motocinsu, kuma hakan ya rage musu ƙarfin kai hari a yankin,” in ji sanarwar.











