Home WASANNI Kocin Najeriya Augustine Eguavoen na Fatan Dawo da Victor Moses

Kocin Najeriya Augustine Eguavoen na Fatan Dawo da Victor Moses

Kocin Najeriya Augustine Eguavoen na Fatan Dawo da Victor Moses

Mai horas da tawagar Super Eagles Augustine Eguavoen na son janyo hankalin tsohon dan wasan Chelsea Victor Moses ya koma bugawa kasarsa da za ta halarci Qatar 2022.

Dan wasan mai shekara 31 da ke taka leda a kungiyar Spartak Moscow da ke Rasha, ya ajiye takalmansa ne a 2018.

Shugaban Hukumar Kwallom Kafa ta Najeriya (NFF) Amaju Pinnick da tsohon kocin Najeriya Gernot Rohr duka sun yi kokarin dawo da dan wasan amma hakarsu ba ta cimma ruwa ba.

Sai dai Eguavoen, wanda ya gaji Rohr a watan Disamba ya ce: “muna son kasarmu ta yi abin arziki.

“Ina son kwallon Victor Moses kuma ina ta kokarin dawo da shi ya ci gaba da bugawa kasarmu.

“Baya cikin tawagarmu da za ta kara da Ghana domin neman gurbi a gasar cin kofin duniya, amma muna sa ran ganinsa a gaba saboda muna son kasar ta yi abin arziki.

“Ko kana so ko baka so yana da gudunmuwar da zai iya bayarwa. Amma a yanzu yana wasa a Rasha, kuma mun san duk matsalar da take faruwa tsakanin Rasha da Ukrain. Cikin farin ina sanar da cewa tattaunawarmu da shi ta fara nisa.”

Moses ya koma Spartak daga Chelsea a 2021, sai dai zai iya sauya kungiya a makonni masu zuwa

Fifa ta shaida wa duk wasu ‘yan wasa da ke taka leda a Rasha su dakatar da kwataraginsu da kasar su kuma fice cikin kankanin lokaci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp