Home WASANNI Kocin Najeriya Augustine Eguavoen na Fatan Dawo da Victor Moses

Kocin Najeriya Augustine Eguavoen na Fatan Dawo da Victor Moses

Kocin Najeriya Augustine Eguavoen na Fatan Dawo da Victor Moses

Mai horas da tawagar Super Eagles Augustine Eguavoen na son janyo hankalin tsohon dan wasan Chelsea Victor Moses ya koma bugawa kasarsa da za ta halarci Qatar 2022.

Dan wasan mai shekara 31 da ke taka leda a kungiyar Spartak Moscow da ke Rasha, ya ajiye takalmansa ne a 2018.

Shugaban Hukumar Kwallom Kafa ta Najeriya (NFF) Amaju Pinnick da tsohon kocin Najeriya Gernot Rohr duka sun yi kokarin dawo da dan wasan amma hakarsu ba ta cimma ruwa ba.

Sai dai Eguavoen, wanda ya gaji Rohr a watan Disamba ya ce: “muna son kasarmu ta yi abin arziki.

“Ina son kwallon Victor Moses kuma ina ta kokarin dawo da shi ya ci gaba da bugawa kasarmu.

“Baya cikin tawagarmu da za ta kara da Ghana domin neman gurbi a gasar cin kofin duniya, amma muna sa ran ganinsa a gaba saboda muna son kasar ta yi abin arziki.

“Ko kana so ko baka so yana da gudunmuwar da zai iya bayarwa. Amma a yanzu yana wasa a Rasha, kuma mun san duk matsalar da take faruwa tsakanin Rasha da Ukrain. Cikin farin ina sanar da cewa tattaunawarmu da shi ta fara nisa.”

Moses ya koma Spartak daga Chelsea a 2021, sai dai zai iya sauya kungiya a makonni masu zuwa

Fifa ta shaida wa duk wasu ‘yan wasa da ke taka leda a Rasha su dakatar da kwataraginsu da kasar su kuma fice cikin kankanin lokaci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp