Home WASANNI Newcastle United na Son Daukar Neymar Daga PSG

Newcastle United na Son Daukar Neymar Daga PSG

Newcastle United na Son Daukar Neymar Daga PSG

 

An ruwaito cewar Newcastle United na duba hanyar da za ta dauko Neymar daga Paris St Germain a karshen kakar bana.

Newcastle wadda aka sayar da ita, ta saka kudi mai tsoka wajen sayo ‘yan wasan da za su kara karfin kungiyar, ciki har da dan kwallon Brazil, Neymar da take son dauka a karshen kakar nan.

Kamar yadda The Sun ta wallafa, Newcastle na bibiyar halin da Neymar ke ciki a PSG, tana kuma son yi masa tayin kudi mai tsoka, domin ya koma buga gasar Premier League.

Bayan da aka yi waje da PSG daga Champions League a bana a hannun Real Madrid, magoya bayan kungiyar Faransa kan yi wa wasu ‘yan wasan ihu a lokacin da suke buga mata leda, ciki har da Neymar.

Tun farko Neymar bai samu alaka mai kyau da PSG da kuma magoya bayanta ba, duk da kwazon da yake yi wa kungiyar, hakan ne Newcastle taga ya dace ta yi wa dan wasan Brazil tayin kudi mai tsoka, watakila ya samu buga babbar gasar tamaula ta Ingila cikin natsuwa.

Neymar yana da kunshin yarjejeniya da PSG wadda za ta kare a karshen kakar 2025, ana kuma ganin Newcastle za ta iya biyan albashin dan wasan na Yuro 500,000 duk mako idan ya amince ya koma kungiyar da taka leda.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp