Home WASANNI Newcastle United na Son Daukar Neymar Daga PSG

Newcastle United na Son Daukar Neymar Daga PSG

Newcastle United na Son Daukar Neymar Daga PSG

 

An ruwaito cewar Newcastle United na duba hanyar da za ta dauko Neymar daga Paris St Germain a karshen kakar bana.

Newcastle wadda aka sayar da ita, ta saka kudi mai tsoka wajen sayo ‘yan wasan da za su kara karfin kungiyar, ciki har da dan kwallon Brazil, Neymar da take son dauka a karshen kakar nan.

Kamar yadda The Sun ta wallafa, Newcastle na bibiyar halin da Neymar ke ciki a PSG, tana kuma son yi masa tayin kudi mai tsoka, domin ya koma buga gasar Premier League.

Bayan da aka yi waje da PSG daga Champions League a bana a hannun Real Madrid, magoya bayan kungiyar Faransa kan yi wa wasu ‘yan wasan ihu a lokacin da suke buga mata leda, ciki har da Neymar.

Tun farko Neymar bai samu alaka mai kyau da PSG da kuma magoya bayanta ba, duk da kwazon da yake yi wa kungiyar, hakan ne Newcastle taga ya dace ta yi wa dan wasan Brazil tayin kudi mai tsoka, watakila ya samu buga babbar gasar tamaula ta Ingila cikin natsuwa.

Neymar yana da kunshin yarjejeniya da PSG wadda za ta kare a karshen kakar 2025, ana kuma ganin Newcastle za ta iya biyan albashin dan wasan na Yuro 500,000 duk mako idan ya amince ya koma kungiyar da taka leda.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp