Home Labarai ‘Yan Sanda a Jihar Zamfara Sun Sami Nasarar Kubutar da Mutane 39...

‘Yan Sanda a Jihar Zamfara Sun Sami Nasarar Kubutar da Mutane 39 da Hannun ‘Yan Bindiga

Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya ta sami nasarar kubutar da mutum 39 Mafi yawan su mata da kananan Yara da ‘Yan Bindiga sukayi garkuwa dasu a  jihar Zamfara.

Kakakin hukumar ‘Yan Sandan Jihar ta Zamfara Muhammad Shehu, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa, inda yace wadanda aka kubutar din na cikin wadanda ‘Yan bindigar sukayi garkuwa dasu a kauyukan dake kananan hukumomin Maru da Bungudu.

“Wadanda aka kubutar sun hadarda Maza 8 Mata 15 cikin su harda masu shayarwa da kuma kananan yara 16” a cewar sa.

“Nasarar ta biyo bayan wani aikin share fage da Rundunar ‘Yan Sanda hadin Gwuiwa da Rundunar Soji suka gudanar a sansanin Dabar Magaji dake dajin Kadanya wanda ke tsakanin Kananan Hukumomin Kaura Namoda da Maradun.

Ya kara da cewa, “ ‘Yan sanda da hadin gwuiwar kungiyar likitocin Gwamnatin Jihar sun dukufa domin bawa wadanda aka ceto kulawa ta musamman, inda daga bisani kuma za’a mika su ga iyalan su, a cewar sa.

Rundunar ‘Yan Sandan ta ce ta sami nasarar kame wasu mutum 10 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban daga cikin su akwai ‘yan haramtacciyar kungiyar ‘yan Sakai.

Yan Sakai kungiya ce ta ‘Yan banga da ke aiki a cikin yankin Arewa Maso Yamma, yawancin su mafarauta ne da ke aiki da Jami’an tsaro don kare Al’ummarsu daga ‘Yan fashin da ke kai farmaki a kauyuka da gonaki.

Daga cikin mutane goman da rundunar ta sami nasarar kamawa akwai mutum 3 da ake zargi da yin garkuwa da mutane 2 a unguwar fakon Idi dake talata mafarada kuma wasu mutane 2 da aka kama da laifin shiga gidaje da satar wayoyin hannu a Gusau babban birnin jihar ta Zamfara.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp