Home Labarai NYSC ta Samar da Sabbin Gidajen Radiyo da TV

NYSC ta Samar da Sabbin Gidajen Radiyo da TV

Tsohon Shugaban Mulkin Soji Yakubu Gowon ya kaddamar da sabbin Gidajen Radiyo da Talabishin mallakin hukumar kula da Masu Yiwa Kasa Hidima ta NYSC.

Gidan Radiyon na NYSC mai mita 88.3 fm da kuma gidan TV dake ka channel 365 akan TSTV.

Kaddamar da tashoshin da ya gudana a harabar hukumar kula da masu yiwa kasa hidima ta NYSC ya sami halartar tsohon shugaban Najeriya Janar Yakubu Gowon, Ministan Wasanni da Matasa Sunday Dare, Tsoffin Daraktocin Hukumar, masu rike da sarautun gargajiya da sauran manyan mutane a fadin Nijeriya.

A jawabin sa, Yakubu Gowon ya yaba da kokarin Janar Shu’aibu Ibrahim, wanda karkashin shugabancin sa ne wannan hukuma ta sami gagarumar nasarar kafa gidan Radiyo da Talabishin.

Tun bayan kafa wannan hukuma tsahon shekaru 49, ta ciga da yaye matasa masu nagarta wanda ke kai kasar ga tudun muntsira.

Da yake jawabi tun da fari Babban Daraktan Hukumar Janar Shu’aibu, ya bayyana cewa samar da kafafen yada labaran na Radiyo da talabishin na matsayin wani bangare na inganta ayyukan hidimar kasar.

Yace dukkan kafafen na NYSC Radio da NYSC TV Mambobin hukumar hidimar kasar ne za suke sarrafasu da kuma wasu cikin ma’aikatan hukumar; haka kuma masu hidimar kasa dake da Muradin samun ilimi a fannin na aikin yada labarai suma suna da dama a kafafen.

By PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp