Home Labarai E-TICKETING: Gwamnatin Tarayya ta Sami Karin Miliyan 3 na Harajin Jirgin Kasa

E-TICKETING: Gwamnatin Tarayya ta Sami Karin Miliyan 3 na Harajin Jirgin Kasa

Ministan Sufuri Rotimi Amaechi yace an dakatar da Hukumar Lura da Sufurin Jiragen Kasa ta Nijeriya (NRC) daga sayar da tikitin hawa Jirgin ga matafiya.

Ya bayyanna hakan ne yayin da yake gabatar da takardar sahelewar saida tikitin da za’a sayar ta yanar gizo (E-ticketing) na Legas zuwa Ibadan dana Itakpe zuwa Warri ga hukumar ICRC

Ameachi Yace an dauki wannan mataki ne domin dakile cin hanci da rashawa da kuma barazanar rashin tsaro da Hukumar ta NRC ke fuskanta.

Ya kara da cewa tun bayan kaddamar da wannan tsari na E-Ticketing kudin shigar da ake samu ya rubanya.

PRNigeria ta rawaito Ameachi na cewa daukar wannan mataki ya zama waji ne kasancewar yadda matsalar rashin tsaro ke kara addabar hanyoyi a Nijeriya

“Duk da dai baza mu iya magance matsalar rashin tsaron da cin hanci da rashawa dari bisa dari ba, amma hakan zai rage matsalar rashin tsaron da muke fuskanta”

“yanzu gwamnatin Tarayya taga Alfanun wannan tsari, ta hanyar kara samun kudin shiga daga miliyan dari daya duk wata zuwa miliyan dari 4.”

Idan za’a iya tunawa PRNigeria ta rawaito cewa wasu ‘Yan Bindiga sun dasa abun fashewa a kan titin jirgin kasa daga Abuja zuwa kaduna Abinda yayi sanadiyyar mutuwar mutane da dama tare da batan wasu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp