Home Labarai E-TICKETING: Gwamnatin Tarayya ta Sami Karin Miliyan 3 na Harajin Jirgin Kasa

E-TICKETING: Gwamnatin Tarayya ta Sami Karin Miliyan 3 na Harajin Jirgin Kasa

Ministan Sufuri Rotimi Amaechi yace an dakatar da Hukumar Lura da Sufurin Jiragen Kasa ta Nijeriya (NRC) daga sayar da tikitin hawa Jirgin ga matafiya.

Ya bayyanna hakan ne yayin da yake gabatar da takardar sahelewar saida tikitin da za’a sayar ta yanar gizo (E-ticketing) na Legas zuwa Ibadan dana Itakpe zuwa Warri ga hukumar ICRC

Ameachi Yace an dauki wannan mataki ne domin dakile cin hanci da rashawa da kuma barazanar rashin tsaro da Hukumar ta NRC ke fuskanta.

Ya kara da cewa tun bayan kaddamar da wannan tsari na E-Ticketing kudin shigar da ake samu ya rubanya.

PRNigeria ta rawaito Ameachi na cewa daukar wannan mataki ya zama waji ne kasancewar yadda matsalar rashin tsaro ke kara addabar hanyoyi a Nijeriya

“Duk da dai baza mu iya magance matsalar rashin tsaron da cin hanci da rashawa dari bisa dari ba, amma hakan zai rage matsalar rashin tsaron da muke fuskanta”

“yanzu gwamnatin Tarayya taga Alfanun wannan tsari, ta hanyar kara samun kudin shiga daga miliyan dari daya duk wata zuwa miliyan dari 4.”

Idan za’a iya tunawa PRNigeria ta rawaito cewa wasu ‘Yan Bindiga sun dasa abun fashewa a kan titin jirgin kasa daga Abuja zuwa kaduna Abinda yayi sanadiyyar mutuwar mutane da dama tare da batan wasu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp