Home Labarai NYSC ta Samar da Sabbin Gidajen Radiyo da TV

NYSC ta Samar da Sabbin Gidajen Radiyo da TV

Tsohon Shugaban Mulkin Soji Yakubu Gowon ya kaddamar da sabbin Gidajen Radiyo da Talabishin mallakin hukumar kula da Masu Yiwa Kasa Hidima ta NYSC.

Gidan Radiyon na NYSC mai mita 88.3 fm da kuma gidan TV dake ka channel 365 akan TSTV.

Kaddamar da tashoshin da ya gudana a harabar hukumar kula da masu yiwa kasa hidima ta NYSC ya sami halartar tsohon shugaban Najeriya Janar Yakubu Gowon, Ministan Wasanni da Matasa Sunday Dare, Tsoffin Daraktocin Hukumar, masu rike da sarautun gargajiya da sauran manyan mutane a fadin Nijeriya.

A jawabin sa, Yakubu Gowon ya yaba da kokarin Janar Shu’aibu Ibrahim, wanda karkashin shugabancin sa ne wannan hukuma ta sami gagarumar nasarar kafa gidan Radiyo da Talabishin.

Tun bayan kafa wannan hukuma tsahon shekaru 49, ta ciga da yaye matasa masu nagarta wanda ke kai kasar ga tudun muntsira.

Da yake jawabi tun da fari Babban Daraktan Hukumar Janar Shu’aibu, ya bayyana cewa samar da kafafen yada labaran na Radiyo da talabishin na matsayin wani bangare na inganta ayyukan hidimar kasar.

Yace dukkan kafafen na NYSC Radio da NYSC TV Mambobin hukumar hidimar kasar ne za suke sarrafasu da kuma wasu cikin ma’aikatan hukumar; haka kuma masu hidimar kasa dake da Muradin samun ilimi a fannin na aikin yada labarai suma suna da dama a kafafen.

By PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp