Home Labarai NYSC ta Samar da Sabbin Gidajen Radiyo da TV

NYSC ta Samar da Sabbin Gidajen Radiyo da TV

Tsohon Shugaban Mulkin Soji Yakubu Gowon ya kaddamar da sabbin Gidajen Radiyo da Talabishin mallakin hukumar kula da Masu Yiwa Kasa Hidima ta NYSC.

Gidan Radiyon na NYSC mai mita 88.3 fm da kuma gidan TV dake ka channel 365 akan TSTV.

Kaddamar da tashoshin da ya gudana a harabar hukumar kula da masu yiwa kasa hidima ta NYSC ya sami halartar tsohon shugaban Najeriya Janar Yakubu Gowon, Ministan Wasanni da Matasa Sunday Dare, Tsoffin Daraktocin Hukumar, masu rike da sarautun gargajiya da sauran manyan mutane a fadin Nijeriya.

A jawabin sa, Yakubu Gowon ya yaba da kokarin Janar Shu’aibu Ibrahim, wanda karkashin shugabancin sa ne wannan hukuma ta sami gagarumar nasarar kafa gidan Radiyo da Talabishin.

Tun bayan kafa wannan hukuma tsahon shekaru 49, ta ciga da yaye matasa masu nagarta wanda ke kai kasar ga tudun muntsira.

Da yake jawabi tun da fari Babban Daraktan Hukumar Janar Shu’aibu, ya bayyana cewa samar da kafafen yada labaran na Radiyo da talabishin na matsayin wani bangare na inganta ayyukan hidimar kasar.

Yace dukkan kafafen na NYSC Radio da NYSC TV Mambobin hukumar hidimar kasar ne za suke sarrafasu da kuma wasu cikin ma’aikatan hukumar; haka kuma masu hidimar kasa dake da Muradin samun ilimi a fannin na aikin yada labarai suma suna da dama a kafafen.

By PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp