Home Labarai Buhari na Ganawa da Tsoffin Shuwagabannin Najeriya

Buhari na Ganawa da Tsoffin Shuwagabannin Najeriya

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na jagorantar taron Majalisar Magaba a fadar Aso Rock dake birnin tarayya Abuja ranar Alhamis.

PRNigeria ta hangi Tsoffin Shugabannin Nijeriya da suka hadar da Janar Abdulsammi Abubakar (rtd) Dr. Goodluck Jonathan, da kuma Janar Yakubu Gowon (rtd), taron da aka fara karfe goma an gudanar da shine a zahiri da kuma kafar internet.

Wannan shine karo na hudu da shugaban ke jagorantar taron. An gudanar da taron farko ne a ranar 21 ga Oktoban, 2015, inda aka gudanar da karon na biyu ranar 7 ga Satumbar 2016 yayin da karo na uku ya kasance a watan August 2020.

Haka kuma sauran wadanda suka sami halartar taron sun hadar da Mataimakin Shugaban Kasa Farfesa Yemi Osibanjo, Sakataren Gwamnatin Tarayya Boss Mustapha, Mai Bawa Shugaban Kasa Shawara a sabgar tsaro Babagana Monguno, da kuma Shugaban Ma’aikatar Fadar Shugaban Kasa Farfesa Ibrahim Gambari.

Gwamnonin da suka sami halartar taron sun hadar da Gwamnan Jihar Imo Hope Uzodinma, Gwamnan Jihar Ekiti Kayode Fayemi, Gwamnan jihar Kebbi Atiku Bagudu, Gwamnan jihar Zamfara Bello Matawalle sai kuma Gwamnan jihar Kaduna Nasir El’Rufa’i.

Kafin fara taron Majalisar Magabatan tayi shiru na minti daya don girmama ga tsohon shugaban Gwamnatin rikon kwarya, Earnest Shonekan, wanda ya rasu a 11 ga watan janairun 2022.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp