Home Labarai Buhari na Ganawa da Tsoffin Shuwagabannin Najeriya

Buhari na Ganawa da Tsoffin Shuwagabannin Najeriya

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na jagorantar taron Majalisar Magaba a fadar Aso Rock dake birnin tarayya Abuja ranar Alhamis.

PRNigeria ta hangi Tsoffin Shugabannin Nijeriya da suka hadar da Janar Abdulsammi Abubakar (rtd) Dr. Goodluck Jonathan, da kuma Janar Yakubu Gowon (rtd), taron da aka fara karfe goma an gudanar da shine a zahiri da kuma kafar internet.

Wannan shine karo na hudu da shugaban ke jagorantar taron. An gudanar da taron farko ne a ranar 21 ga Oktoban, 2015, inda aka gudanar da karon na biyu ranar 7 ga Satumbar 2016 yayin da karo na uku ya kasance a watan August 2020.

Haka kuma sauran wadanda suka sami halartar taron sun hadar da Mataimakin Shugaban Kasa Farfesa Yemi Osibanjo, Sakataren Gwamnatin Tarayya Boss Mustapha, Mai Bawa Shugaban Kasa Shawara a sabgar tsaro Babagana Monguno, da kuma Shugaban Ma’aikatar Fadar Shugaban Kasa Farfesa Ibrahim Gambari.

Gwamnonin da suka sami halartar taron sun hadar da Gwamnan Jihar Imo Hope Uzodinma, Gwamnan Jihar Ekiti Kayode Fayemi, Gwamnan jihar Kebbi Atiku Bagudu, Gwamnan jihar Zamfara Bello Matawalle sai kuma Gwamnan jihar Kaduna Nasir El’Rufa’i.

Kafin fara taron Majalisar Magabatan tayi shiru na minti daya don girmama ga tsohon shugaban Gwamnatin rikon kwarya, Earnest Shonekan, wanda ya rasu a 11 ga watan janairun 2022.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp