Home Labarai Buhari na Ganawa da Tsoffin Shuwagabannin Najeriya

Buhari na Ganawa da Tsoffin Shuwagabannin Najeriya

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na jagorantar taron Majalisar Magaba a fadar Aso Rock dake birnin tarayya Abuja ranar Alhamis.

PRNigeria ta hangi Tsoffin Shugabannin Nijeriya da suka hadar da Janar Abdulsammi Abubakar (rtd) Dr. Goodluck Jonathan, da kuma Janar Yakubu Gowon (rtd), taron da aka fara karfe goma an gudanar da shine a zahiri da kuma kafar internet.

Wannan shine karo na hudu da shugaban ke jagorantar taron. An gudanar da taron farko ne a ranar 21 ga Oktoban, 2015, inda aka gudanar da karon na biyu ranar 7 ga Satumbar 2016 yayin da karo na uku ya kasance a watan August 2020.

Haka kuma sauran wadanda suka sami halartar taron sun hadar da Mataimakin Shugaban Kasa Farfesa Yemi Osibanjo, Sakataren Gwamnatin Tarayya Boss Mustapha, Mai Bawa Shugaban Kasa Shawara a sabgar tsaro Babagana Monguno, da kuma Shugaban Ma’aikatar Fadar Shugaban Kasa Farfesa Ibrahim Gambari.

Gwamnonin da suka sami halartar taron sun hadar da Gwamnan Jihar Imo Hope Uzodinma, Gwamnan Jihar Ekiti Kayode Fayemi, Gwamnan jihar Kebbi Atiku Bagudu, Gwamnan jihar Zamfara Bello Matawalle sai kuma Gwamnan jihar Kaduna Nasir El’Rufa’i.

Kafin fara taron Majalisar Magabatan tayi shiru na minti daya don girmama ga tsohon shugaban Gwamnatin rikon kwarya, Earnest Shonekan, wanda ya rasu a 11 ga watan janairun 2022.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp