TSARO: Dakarun MNJTF Sun Tarwatsa Maboyar Mayakan ISWAP

Dakarun hadin gwuiwa na MNJTF sun yi Ruwan wuta kan sansanonin horas da mayakan kungiyar tada kayar baya ta Boko Haram tsagin ISWAP  da matsugunnan kwamandojin su a yankin Tafkin Chadi.

Wata majiyar liken asiri ta shaidawa PRNigeria cewa, dakarun sojin kakarshin jagorancin Rundunar Sojin Saman Nijar sun kai harin ne a ranar Alhamis, 14 ga Afrilun, 2022, a Tumbun Rego.

“Wani bayanin sirri ya nuna cewa wurin da aka kai harin ya zama wurin da manyan kwamandojin ISWAP ke zama, harin daya kai ga kawar da  wasu cikin kwamandojin da suka hada da Ibn Usman, Hani Abdullahi, Ababak Shuwa, Abu Jibrilla da Abu Ali.

“tare da hadin Gwuiwa jiragen yaki na Rundunar Sojin Saman Nijar, Jiragen sun kai hari a kusa da wuraren dake zama mafakar mayaka da iyalan ‘Yan Ta’addan.”

“A ranar 15 ga watan Afrilu, 2022 Rundunar Sojojin Nijeriya karkashin Operation Lake Sanity suka gudanar da aikin kawar da ‘Yan ta’addan, inda tuni suka kwace iko da yankuna da dama da ‘Yan ta’addan suke mamaye a dajin Sambisa tare da cigaba da kai musu hare-hare a dajin Tumbun.

“Hare-haren jiragen sama da kuma ayyukan sojojin kasa sun I sanadiyyar mutuwan ‘yan ta’adda da dama inda wasu da dama suka sami muggan raunika

PRNigeria Hausa

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 15 minutes 9 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 56 minutes 34 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com