Dakarun MNJTF Sun Sake Halaka Mayakan ISWAP

Wani Harin Dakarun hadin gwuiwar Rundunar Soji ta MNJTF Ya sake Halaka Mayakan Kungiyar tada kayar baya ta Boko Haram Masu tarin ya Jamhuriyyar Nijar.

Dakarun rundunar hadin gwuiwar ta kasa da kasa MNJTF sun yi nasarar fatattakar ‘Yan ta’addar ne a maboyar mayakan na ISWAP a jamhuriyar Nijar.

PRNigeria ta rawaito cewa ‘yan ta’addan sun gamu da gamon su ne, bayan sun yi yunkurin kai hari wani Depo na Man fetur a garin Soudeye dake yankin Borgogorou a jamhuriyyar Nijar.

A ranar Asabar din data gabata ne dai wani rahoto ya bayyana yadda jami’an tsaro suka fatattaki ‘yan ta’addan, bayan kwashe sama da sa’a guda ana fafatawa, abinda yayi sanadiyyar rayukan ‘yan ta’addan masu tarin yawa.

A dai ‘yan tsakanin na rundunar a wani harin hadin gwuiwa, ta farmaki ‘yan ta’addan ta sama, inda wasu cikin ‘yan ta’adda suka gudu cikin motoci domin tsira da rayukan su.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 17 minutes 10 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 58 minutes 35 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com