Home Labarai Dakarun ‘Yan Sanda Sun Lakadawa Kwamandan Hukumar NSCDC Duka

Dakarun ‘Yan Sanda Sun Lakadawa Kwamandan Hukumar NSCDC Duka

Dakarun Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Imo dauke da Makamai, sun kutsa shalkwatar hukumar tsaro ta Civil Defence (NSCDC) inda suka lakadawa kwamandan hukumar Micheal Ogar dukan kawo wuka.

Rahotan da PrNigeria ta samu ya nuna cewa tuni jami’an ‘Yan Sandan suka halaka mai tsaron lafiyar Kwamandan, bayan da Dakarun Hukumar ta Civil Defence ke kwance cikin muggana raunika.

PRNigeria ta rawaito cewa jami’an ‘Yan Sandan Kwantar da tarzo ta Mobile Police na Squadron – 18 a Jihar ta Imo ne suka aika ta wannan danyen hukunci.

Lamarin dai ya faru ne bayan da kwamandan ya shiga tsakanin wata takaddama daga auku tsakanin jami’in hukumar da wasu jami’an ‘Yan sanda.

Wata sahihiyar majiya ta shaidawa PRNigeria cewa lamarin ya faru tsakanin jami’an inda aka dingi musayar wuta da manyan bindigu a shalkwatar hukumar ta NSCDC dake kusa works layout a Owerri, Babban Birnin Jihar.

Binciken da PrNigeria ta gudanar ya nuna cewa rikicin ya samu asali ne bayan takaddama  mai zafi tsakanin direban kwamandan Hukumar ta NSCDC na  Jihar ta Imo da wani Dan Sanda a kayan gida wanda ya rufe hanyar da kwamandan zai wuce.

Har zuwan lokacin hada wannan rahoto, PRNigeria bata sami nasarar jin ta bakin Kakakin hukumomin guda biyu ba

By PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp