Home Labarai Dakarun ‘Yan Sanda Sun Lakadawa Kwamandan Hukumar NSCDC Duka

Dakarun ‘Yan Sanda Sun Lakadawa Kwamandan Hukumar NSCDC Duka

Dakarun Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Imo dauke da Makamai, sun kutsa shalkwatar hukumar tsaro ta Civil Defence (NSCDC) inda suka lakadawa kwamandan hukumar Micheal Ogar dukan kawo wuka.

Rahotan da PrNigeria ta samu ya nuna cewa tuni jami’an ‘Yan Sandan suka halaka mai tsaron lafiyar Kwamandan, bayan da Dakarun Hukumar ta Civil Defence ke kwance cikin muggana raunika.

PRNigeria ta rawaito cewa jami’an ‘Yan Sandan Kwantar da tarzo ta Mobile Police na Squadron – 18 a Jihar ta Imo ne suka aika ta wannan danyen hukunci.

Lamarin dai ya faru ne bayan da kwamandan ya shiga tsakanin wata takaddama daga auku tsakanin jami’in hukumar da wasu jami’an ‘Yan sanda.

Wata sahihiyar majiya ta shaidawa PRNigeria cewa lamarin ya faru tsakanin jami’an inda aka dingi musayar wuta da manyan bindigu a shalkwatar hukumar ta NSCDC dake kusa works layout a Owerri, Babban Birnin Jihar.

Binciken da PrNigeria ta gudanar ya nuna cewa rikicin ya samu asali ne bayan takaddama  mai zafi tsakanin direban kwamandan Hukumar ta NSCDC na  Jihar ta Imo da wani Dan Sanda a kayan gida wanda ya rufe hanyar da kwamandan zai wuce.

Har zuwan lokacin hada wannan rahoto, PRNigeria bata sami nasarar jin ta bakin Kakakin hukumomin guda biyu ba

By PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp