• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home Labarai VIDEO: Yadda ‘Yan Ta’adda suka kori Mutum Dubu 10 Suka Halaka Mutum...
  • Labarai

VIDEO: Yadda ‘Yan Ta’adda suka kori Mutum Dubu 10 Suka Halaka Mutum Dari 2 a Jihar Kebbi

By
Prnigeria
-
May 3, 2022
Arewa Award

Wani bincike da jaridar PRNigeria ta gudanar ya bayyana cewa akalla mutane dubu 10 ne suka rasa mutsugunnan su  tsahon shekaru 3 da suka gabata, a jihar Kebbi dake Arewacin Nijeriya.

Kalli Video:

Mutanen sun rasa matsugunnin ne sakamakon wasu hare-hare da ‘Yan bindiga suka kaddamar a tsakanin kauyukan Chonoko da wasu yankuna a karamar hukumar Danko/Wasagu ta Jihar.

Jaridar tace wani kisan kiyashi da ‘Yan bindigar suka fara kan Al’ummomin sun halaka mutum 200 tare da fatattakar kauyuka 42 a shekarar 2019.

Kauyukan sun hadar da Dan Kade, Warkata, Kurgiye, Ragam I, II da ta III, ‘Yar Kuka, Shangel, Tungan Dangula, Kahalmo I da ta II, Kadebo, Ched-Kubu, Yababa, Gimi, Ganyale I, II da ta III, Silabi da kuma  Digoga.

Sai kuma wasu kauyukan da suka hadar da; Bankunatare, Bawada, Zagami, Turame, Gyado, Tungan Kwando, Ketare, Sebzama I, II da ta III, Dhilo da kuma Duru.

Sauran sun hadar da; Tudun Wada, Digwengwe, Gaya, Saaki, ‘Yar Buga, Dilanko, Zuttu da Irgaa.

Wakilan jarida su biyu (2) da suka ziyarci garin na Chonoko, sun rawaito cewa tun daga lokacin ‘yan bindigar suka mamaye gidajen wadanda suka mutu ba tare da wani daukar mataki kan hakan ba.

A yayin da yake bayyanawa PRNigeria irin halin da ya shiga, wani tsoho mai kimanin shekaru 70 mai suna Mai Unguwa Maizuwa da aka kora daga kauyen Zagami ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun shafe shekaru 3 a jere suna kai hare-hare a kan al’ummar tun daga shekarar 2019.

Yace “’yan bindigar bayan sun kore shanun su sun kuma yi awon gaba da dukiyoyinsu, baya ga hallaka mutane da dama, sannan kuma a ‘yan tsakanin nan sun kori kowa daga kauyen.

Mai zuwa yace “bayan haka yayi asarar wasu kayayyaki da suka hadar da buhunan siminti da dama da kuma wasu kudade da ya ajiye na kasuwanci, kimanin naira 997,000 a yayin harin

Read Also:

  • Sojojin Najeriya sun kashe ƴanbindiga tare da ceto wasu da aka sace a Borno
  • Nan gaba za ku ga Amfanin dokar haraji -Tinubu
  • Amurka ta fara kai harin soji Arewacin Nijeriya

Mai zuwa dake da ‘ya’ya guda Shirin (20) yanzu haka yana rayuwa ne a sansanin ‘yan gudun hijra mai tarin cunkoso dake garin Chonoko.

Wani magidanci daya rasa Dan sa sakamakon wasu hare-haren ‘Yan bindiga a kauyen Kadebo, Musa Sarkin Makada, ya bayyana wa PRNigeria yadda suka shiga halin kakanakayi tun bayan da akayi awon gaba da Al’ummomin su.

An ruwaito cewa tun da aka kai hare-haren kauyen ya zama tamkar kufai, baya ga kwashe mata da kananan yara da tsoffi gami da nakasassu wadanda baza su iya guduwa ba domin tsira da rayuka su.

Shima da yake Magana a irin wannan yanayi na alhini, guda cikin shugaban al’ummar duk da ya nemi a sakaye sunan sa, ya bayyanawa PRNigeria cewa kawo yanzu ‘yan ta’addan na cigaba da cin karen su babu babbaka ba tare da an hukunta su ba; inda  suka kori wasu mutane da kauyukan su tare da kone  gidaje da kayayyakin abinci inda makarantu suka kasance a rufe.

“Baya ga hare-hare da garkuwa da mutanen kauyen, ‘yan bindigar na lalata gonaki da gidajen al’ummomin yankin da basu da karfi.

“Matsalar abinci da ake fuskanta babu shakka zata lakume rayukan mutane da dama, saboda an tilastawa dubban manoma hakura da gonakin su, kuma hakan ya rage ayyukan noman da ke matsayin hanya daya tilo ga mazauna yankin. Haka kuma an rufe makarantu a dukkan kayukan da al’amarin ya shafa, kaga wannan na taimakawa wajen kara yawan daliban da basu samin damar karatun.

“Bugu da kari, duk wannan ta’asa da ‘yan ta’addan ke aikatawa, babu wasu jami’an tsaro dake kokarin daukar mataki domin magance ayyukan su, yayin da hukumomin agaji da suka hadar da Red Cross da hukumar bada agajin gaggawa ta NEMA basu bayar da wani tallafi ga ‘Yan gudun hijirar musamman kayayyakin agaji da magunguna ga marasa lafiya da masu rauni.

“Yanzu haka dai mutanen da suka rasa matsugunansu basu da Muradin komawa gidajen sakamakon mummunan yanayin da suka fuskanta,” kamar yadda ya bayyana cikin tashin hankali.

A martanin da hukumar bada agajin gaggawa ta NEMA tayi kan wannan rahoto hukumar tayi alkawarin magance matsalolin da ‘yan gudun hijirar ke ciki da gaggawa, yayin da ICRC tace, sakamakon ayyukan jin kai da suke yi a yankin Arewa Maso Gabas da kuma Arewa ta Tsakiya, kawo yanzu da basu sami damar mayar da hankali kan  Arewa Maso Yammacin Nijeriya ba.

By PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
  • TAGS
  • 'Yan Gudun Hijira
  • Chonoko
  • Kebbi
  • NEMA
  • Yan Ta'adda
  • Yara
Previous articleShugaban NITDA ya Halarci Bikin Sallah a Rana ta Biyu a Haɗejia
Next articleGidauniyar Malam Inuwa ta ba da Gudunmawar Mota ga Kungiyar Mata Masu Yaki da Cin Zarafin Mata da Kananan Yara
Prnigeria

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Sojojin Najeriya sun kashe ƴanbindiga tare da ceto wasu da aka sace a Borno

Nan gaba za ku ga Amfanin dokar haraji -Tinubu

Amurka ta fara kai harin soji Arewacin Nijeriya

Sojoji sun daƙile yunƙurin harin ƴanbidiga a Borno

Gwamnatin Nijeriya ta yi watsi da kudirin hukuncin kisa ga masu garkuwa

ADC ta buƙaci a dakatar da aiwatar da sabuwar dokar haraji

Gwamnati Nijeriya ta haramta fitar da itace zuwa ƙasashen waje

Tinubu ya maye gurbin Engr Farouk daga shugabancin hukumar NMDPRA

ICPC ta ce zata binciki shugaban hukumar NMDPRA

Za mu ci gaba da kamen masu bakin gilashin mota – Yan sanda

Majalisa ta amince da naɗin sabbin jakadun da Tinubu ya gabatar

Gwamnan Kano Ya Kafa Runduna ta Musamman Don Tabbatar da Tsaro a Tashoshin Mota

Recent Posts

  • Sojojin Najeriya sun kashe ƴanbindiga tare da ceto wasu da aka sace a Borno
  • Nan gaba za ku ga Amfanin dokar haraji -Tinubu
  • Amurka ta fara kai harin soji Arewacin Nijeriya
  • Sojoji sun daƙile yunƙurin harin ƴanbidiga a Borno
  • Gwamnatin Nijeriya ta yi watsi da kudirin hukuncin kisa ga masu garkuwa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1664 days 9 hours 42 minutes 8 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1646 days 11 hours 23 minutes 33 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Sojojin Najeriya sun kashe ƴanbindiga tare da ceto wasu da aka sace a BornoNan gaba za ku ga Amfanin dokar haraji -TinubuAmurka ta fara kai harin soji Arewacin NijeriyaSojoji sun daƙile yunƙurin harin ƴanbidiga a BornoGwamnatin Nijeriya ta yi watsi da kudirin hukuncin kisa ga masu garkuwaADC ta buƙaci a dakatar da aiwatar da sabuwar dokar harajiGwamnati Nijeriya ta haramta fitar da itace zuwa ƙasashen wajeTinubu ya maye gurbin Engr Farouk daga shugabancin hukumar NMDPRAICPC ta ce zata binciki shugaban hukumar NMDPRAZa mu ci gaba da kamen masu bakin gilashin mota - Yan sandaMajalisa ta amince da naɗin sabbin jakadun da Tinubu ya gabatarShugaban Najeriya zai iya dakatar da gwamna - Kotun ƘoliGwamnan Kano Ya Kafa Runduna ta Musamman Don Tabbatar da Tsaro a Tashoshin MotaNNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar DeltaKotun Ƙolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kisa kan Maryam Sanda
X whatsapp