Home Labarai ISWAP Ta Hallaka Tsohon Mashawarci Ga Abubakar Shekau

ISWAP Ta Hallaka Tsohon Mashawarci Ga Abubakar Shekau

Kungiyar ta da kayar baya ta Boko Haram tsagin ISWAP, sun hallaka tsohon mataimaki na musamman ga Abubakar Shekau, bayan yayi kokarin mika wuya.

Jaridar PRNigeria ta rawaito cewa mayakan na ISWAP sun halaka Abu-sadiq Burbur, bisa zargin sa da shirin mika wuya ga Dakarun Rundunar Sojin Nijeriya.

Wata Majiya mai tushe ta shaidawa PRNigeria cewa an halaka Burbur ne a kauyen Galta da ke kusa da Madagali bayan kungiyar ISWAP ta tuhume shi da laifin cin amanar kasa.

inda daga bisani aka gurfanar da shi a wata kotun masu tada kayar dake zaman ta a dajin Sambisa wadda Ya-shaik guda cikin mayakan na ISWAP ke jagoranta.

Burbur dai tsohon mashawarci ne ga tsohon shugaban kungiyar Boko Haram Abubakar shekau.

Ana dai kallon wannan lamari na mika wuya da mayakan na kungiyoyin tada kayar bayan ke yi a ‘yan tsakanin nan nada nasaba da ruwan wuta gami da farmaki da dakarun sojin ke kai musu babu kakkautawa a maboyar su

 

By PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp