Home Labarai Kwamandan Sojoji Ya Bace Bayan Dakarun Sojoji Sun Kashe Mayakan ISWAP Da...

Kwamandan Sojoji Ya Bace Bayan Dakarun Sojoji Sun Kashe Mayakan ISWAP Da Dama A Jihar Taraba.

Dakarun Sojin Nijeriya sun sami nasarar halaka wasu da ake zargin ‘ya’ya kungiyar tada kayar baya na Boko Haram ne tsagin ISWAP a Jihar Taraba kamar yadda jaridar PRNigeria ta rawaito.

Mayakan na Kungiyar ta ISWAP sun gamu da ajalin nasu ne a yayin da suka farwa sojojin dake wani samame a Kauyen Tati dake Karamar Hukumar Takum a Jihar.

Sai dai wani rahato ya bayyana cewa Kwamandan dake jagorantar bataliya ta 93 yayi batan dabo kama yadda Jarida ta PRNigeria ta ruwaito.

A kalla Sojoji 6 ne suka rasa rayukan su yayin artabun, sai dai rahoton yace sojin sun sami nasarar halaka ‘yan ta’addan masu tarin yawa.

Wata majiya daga Rundunar Sojin ta tabbatar da cewa an nemi Kwamandan da guda cikin masu taimaka masa an rasa, duk da dai sojojin a yain musayar wutar sun sami nasarar halaka ‘yan bindigar da dama.

“ta cikin wasu mabambanta hare-hare da sojojin suka kai sun sami nasarar halaka mayakan ISWAP a kauyen Ananum dake Donga a wani shinge da kuma mararraba bisa taimakon wasu dakarun sojin.

By PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp