Home Labarai Kwamandan Sojoji Ya Bace Bayan Dakarun Sojoji Sun Kashe Mayakan ISWAP Da...

Kwamandan Sojoji Ya Bace Bayan Dakarun Sojoji Sun Kashe Mayakan ISWAP Da Dama A Jihar Taraba.

Dakarun Sojin Nijeriya sun sami nasarar halaka wasu da ake zargin ‘ya’ya kungiyar tada kayar baya na Boko Haram ne tsagin ISWAP a Jihar Taraba kamar yadda jaridar PRNigeria ta rawaito.

Mayakan na Kungiyar ta ISWAP sun gamu da ajalin nasu ne a yayin da suka farwa sojojin dake wani samame a Kauyen Tati dake Karamar Hukumar Takum a Jihar.

Sai dai wani rahato ya bayyana cewa Kwamandan dake jagorantar bataliya ta 93 yayi batan dabo kama yadda Jarida ta PRNigeria ta ruwaito.

A kalla Sojoji 6 ne suka rasa rayukan su yayin artabun, sai dai rahoton yace sojin sun sami nasarar halaka ‘yan ta’addan masu tarin yawa.

Wata majiya daga Rundunar Sojin ta tabbatar da cewa an nemi Kwamandan da guda cikin masu taimaka masa an rasa, duk da dai sojojin a yain musayar wutar sun sami nasarar halaka ‘yan bindigar da dama.

“ta cikin wasu mabambanta hare-hare da sojojin suka kai sun sami nasarar halaka mayakan ISWAP a kauyen Ananum dake Donga a wani shinge da kuma mararraba bisa taimakon wasu dakarun sojin.

By PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp