Home Labarai ISWAP Ta Hallaka Tsohon Mashawarci Ga Abubakar Shekau

ISWAP Ta Hallaka Tsohon Mashawarci Ga Abubakar Shekau

Kungiyar ta da kayar baya ta Boko Haram tsagin ISWAP, sun hallaka tsohon mataimaki na musamman ga Abubakar Shekau, bayan yayi kokarin mika wuya.

Jaridar PRNigeria ta rawaito cewa mayakan na ISWAP sun halaka Abu-sadiq Burbur, bisa zargin sa da shirin mika wuya ga Dakarun Rundunar Sojin Nijeriya.

Wata Majiya mai tushe ta shaidawa PRNigeria cewa an halaka Burbur ne a kauyen Galta da ke kusa da Madagali bayan kungiyar ISWAP ta tuhume shi da laifin cin amanar kasa.

inda daga bisani aka gurfanar da shi a wata kotun masu tada kayar dake zaman ta a dajin Sambisa wadda Ya-shaik guda cikin mayakan na ISWAP ke jagoranta.

Burbur dai tsohon mashawarci ne ga tsohon shugaban kungiyar Boko Haram Abubakar shekau.

Ana dai kallon wannan lamari na mika wuya da mayakan na kungiyoyin tada kayar bayan ke yi a ‘yan tsakanin nan nada nasaba da ruwan wuta gami da farmaki da dakarun sojin ke kai musu babu kakkautawa a maboyar su

 

By PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp