Home Labarai Kwamandan Sojoji Ya Bace Bayan Dakarun Sojoji Sun Kashe Mayakan ISWAP Da...

Kwamandan Sojoji Ya Bace Bayan Dakarun Sojoji Sun Kashe Mayakan ISWAP Da Dama A Jihar Taraba.

Dakarun Sojin Nijeriya sun sami nasarar halaka wasu da ake zargin ‘ya’ya kungiyar tada kayar baya na Boko Haram ne tsagin ISWAP a Jihar Taraba kamar yadda jaridar PRNigeria ta rawaito.

Mayakan na Kungiyar ta ISWAP sun gamu da ajalin nasu ne a yayin da suka farwa sojojin dake wani samame a Kauyen Tati dake Karamar Hukumar Takum a Jihar.

Sai dai wani rahato ya bayyana cewa Kwamandan dake jagorantar bataliya ta 93 yayi batan dabo kama yadda Jarida ta PRNigeria ta ruwaito.

A kalla Sojoji 6 ne suka rasa rayukan su yayin artabun, sai dai rahoton yace sojin sun sami nasarar halaka ‘yan ta’addan masu tarin yawa.

Wata majiya daga Rundunar Sojin ta tabbatar da cewa an nemi Kwamandan da guda cikin masu taimaka masa an rasa, duk da dai sojojin a yain musayar wutar sun sami nasarar halaka ‘yan bindigar da dama.

“ta cikin wasu mabambanta hare-hare da sojojin suka kai sun sami nasarar halaka mayakan ISWAP a kauyen Ananum dake Donga a wani shinge da kuma mararraba bisa taimakon wasu dakarun sojin.

By PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp