Kwamandan Sojoji Ya Bace Bayan Dakarun Sojoji Sun Kashe Mayakan ISWAP Da Dama A Jihar Taraba.

Dakarun Sojin Nijeriya sun sami nasarar halaka wasu da ake zargin ‘ya’ya kungiyar tada kayar baya na Boko Haram ne tsagin ISWAP a Jihar Taraba kamar yadda jaridar PRNigeria ta rawaito.

Mayakan na Kungiyar ta ISWAP sun gamu da ajalin nasu ne a yayin da suka farwa sojojin dake wani samame a Kauyen Tati dake Karamar Hukumar Takum a Jihar.

Sai dai wani rahato ya bayyana cewa Kwamandan dake jagorantar bataliya ta 93 yayi batan dabo kama yadda Jarida ta PRNigeria ta ruwaito.

A kalla Sojoji 6 ne suka rasa rayukan su yayin artabun, sai dai rahoton yace sojin sun sami nasarar halaka ‘yan ta’addan masu tarin yawa.

Wata majiya daga Rundunar Sojin ta tabbatar da cewa an nemi Kwamandan da guda cikin masu taimaka masa an rasa, duk da dai sojojin a yain musayar wutar sun sami nasarar halaka ‘yan bindigar da dama.

“ta cikin wasu mabambanta hare-hare da sojojin suka kai sun sami nasarar halaka mayakan ISWAP a kauyen Ananum dake Donga a wani shinge da kuma mararraba bisa taimakon wasu dakarun sojin.

By PRNigeria

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 9 minutes 34 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 50 minutes 59 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com