Home Labarai ‘Yan Bindiga Sun Raunata Magidanci Tare Da Yin Awon Gaba Da ‘Dan...

‘Yan Bindiga Sun Raunata Magidanci Tare Da Yin Awon Gaba Da ‘Dan Sa A Abuja

Wasu mahara da ake zargin ‘Yan Bindiga ne sun yi awon gaba da wani matashi mai kimanin shekaru 18 da haihuwa mai suna Victor Egbon a unguwar Zone A dake yankin Kuje a birnin tarayya Abuja, bayan sun raunata mahaifinsa.

Victor da ne ga mamallakin makarantar Supreme Kids Academy, dake birnin tarayyar Nijeriya.

An rawaito cewa an garzaya da mahaifin matashin mai suna Abdulsalam Ozigi asibiti sakamakon mugun raunin da ‘yan ta’addar suka ji masa a jikin shi.

Wani shaidar gani da ido da ya nemi a sakayi sunan sa, yace ‘yan bindigar sun kai farmaki gidan Ozigi da misalin karfe 12:15 na daren litinin, inda suka yi awon gaba da Victor bayan sun lalata wasu kofofin gidan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp