Home Labarai Gwamnatin Nijeriya Tace Ba za tayi Amfani Da Karfi Ba Wajen Karbo...

Gwamnatin Nijeriya Tace Ba za tayi Amfani Da Karfi Ba Wajen Karbo Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja Zuwa Kaduna Ba

Fadar shugaban kasa tace ‘yan ta’addan da suka yi garkuwa da jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna sun yaudari Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta hanyar gaza cika Alkawarin da suka dauka duk da cewa gwamnatin tarayya ta biya musu bukatun su.
Mai Magana da yawun shugaban kasar Garba Shehu ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai.
Garba Shehu yace gwamnatin tarayya ta cika wa jagoran ‘yan ta’addan Alkawarin data dauka na sakin matar sa dake da ciki, amma daga bisani ya karya Alkawarin daya dauka.
Lokacin da suke tattaunawar sulhu da Gwamnatin tarayya, sun yi alkawarin sakin fasinjojin jirgin da suka yi garkuwa dasu amma masu garkuwar sun gaza cika Alkawarin da suka dauka.
Garba shehu yace bayan gwamantin tarayya ta sauki alkawarin data dauka daga bangaren ta, su kuma ‘yan bindigar suka zo da wani sabon salon yaudara.
Wannan dai na zuwa ne sa’oi kadan bayan da shugabanin Nijeriya Muhammadu Buhari ya gana da fasinjojin da ‘yan bindigar suka sako a fadar gwamnatin tarayya a ranar Alhamis.
Garba shehu ya kara da cewa ba wannan karon farko da ‘yan ta’addan ke saba alkawarin da suka dauka ba, amma wannan ne karon farko da gwamnatin tarayya ta bayyana abinda ke faruwa ga Al’ummar kasa tsakanin ta da ‘yan bindigar.
Yanzu haka dai akwai sauran fasinjoji 31 da suka rage a hannun ‘yan ta’addan a daji, amma gwamnatin tarayyar tace baza tayi amfani da karfin tuwo ba domin karbo su, saboda tana bukatar karbo su a raye.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp