Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara tace mutum bakwai 7 ‘yan gida daya ne suka mutu sakamakon cin dambu a matsayin abinci dare a jihar
Kakakin rundunar SP Mohammad shehu ne ya bayyana hakan ga manema labarai, cewa rundunar na kan bincike kan lamarin, domin gano musabbabin mutuwar mutane ‘yan kauyen Danbaza dake karamar hukumar Maradun.
Read Also:
“lamarin ya auku ne ranar litinin bayan iyalan sun ci wani abinci da suka girka a matsyain abinci dare.
“Mun dauki samfurin abincin da suka ci, kuma ana kan bincike, da zarar an kamala kuma zamu sanar da manema labarai,” a cewar Muhammad Shehu.
Wani mazaunin kauyen muhamma Kabir kuma makusance ga mamatan ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Nijeriya cewa hudu cikin wadanda suka mutun 2 matan aure ne sun mutu nan take, yayin da 5 kuma sai da aka garzaya da su asibiti, kafin suka ce ga garin ku nan.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 14 hours 49 minutes 33 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 16 hours 30 minutes 58 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com