An Ceto Wasu Cikin Wadanda Gini Ya Ruftawa a Kano – Gwamnatin Jihar

Gwamnatin jihar Kano ta bada tabbacin ceto wasu mutane cikin wadanda gini ya rufta kan su a jihar dake Arewacin.

Mataimakin Gwamnan jihar Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ne ya bayyana hakan yayin da yakai ziyarar gani da ido wurin da lamarin ya faru, a kasuwar sayar da waya wayoyin hannu dake titin Beirut a jihar dake Arewacin Nijeriya.

Gwamnatin jihar ta bakin mataimakin gwamnan ta nuna kaduwar ta kan iftila’in, tare da jan hankalin Al’ummar da suka je wajen kallo dasu gaggauta barin wajen domin bawa masu aikin damar ceto wadanda ke karkashin gini, daga bisani ya jajantawa wadanda lamarin ya rutsa dasu.

Tun da fari dai an ruwaito cewa ginin ya ruf ta kan mutanen ne a yammacin wannan rana wanda kuma yanzu haka ana aikin ceto mutanen da suka makale.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 30 minutes 12 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 11 minutes 37 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com