Home General Ana Fargabar Gini Ya Rufta Kan Mutane Da Dama A Jihar Kano

Ana Fargabar Gini Ya Rufta Kan Mutane Da Dama A Jihar Kano

Rahotanni daga kasuwar sayar da wayoyin hannu dake titin beirut a birnin kano dake Arewacin Nijeriya, na cewa wani bene ya rufta kuma ana tsammanin ya danne mutane da dama.
shaidun gani da ido sun shaidawa wakilan mu cewa, yanzu haka ana cen ana kokarin ceto wadanda ke karkashin baraguzai, yayin da aka garzaya da wadanda suka ji rauni asibiti.
Ko dai a ‘yan tsakanin nan Wani ginin bene mai hawa uku da ake aikin ginisa ya rufta a unguwar Kubwa da ke Abuja babban birnin tarayyar Najeriya.
Faduwar ginin dai ya rutsa da mutanen bakwai a ciki inda jami’an biyu daga cikinsu suka mutu yayin da jami’an hukumar kai daukin gaggawa ta Abuja suka samu ceto mutane biyar daga baraguzan ginin.
Ba kasafai aka fiya samun ruftawar gini a jihar ba, duk da cewa dai shaidun gani da ido sun dora alhakin rushewar kan rashin ingancin kayan aikin gini.
Kawo yanzu dai hukumomi a jihar basu ce kamai kan wannan lamarin ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp