Home Labarai Sojoji Sun Ceto Basaraken Gargajiya na Plateau da Aka yi Garkuwa da...

Sojoji Sun Ceto Basaraken Gargajiya na Plateau da Aka yi Garkuwa da shi

Sojoji Sun Ceto Basaraken Gargajiya na Plateau da Aka yi Garkuwa da shi

 

Wani basaraken gargajiya na kauyen Pinau da ke karamar hukumar Wase a jihar Filato, Dokta Dadda’u Ahmad, wanda aka yi garkuwa da shi da sanyin safiyar Talata tare da direbansa, sojojin da ke aiki da rundunar ‘Operation Safe Haven’ a kauyen sun ceto shi.

Kakakin rundunar ‘Operation Safe Haven’ da ke aikin tabbatar da zaman lafiya a Filato da Bauchi da wasu sassan Karina Manjo Ishaku Takwa ya tabbatar da faruwar lamarin.

Wani mazaunin kauyen Hassan Pinau ya ce, wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da basaraken gargajiya da aka ceto tare da direbansa a hanyarsu ta zuwa Wase.

Ya bayyana cewa jim kadan bayan samun labarin faruwar lamarin ga sojoji a kauyen, sai suka zage damtse tare da bin diddigin masu garkuwa da mutanen inda suka kwato bindigogi biyu, da babura uku.

Musa Hassan, wani ma’aikacin da ke kula da unguwanni a yankin, ya shaida wa jaridar The Nation cewa: “Ina tare da sojoji a lokacin aikin ceto. Sojoji da wasu ’yan unguwar ne suka dawo da basaraken gargajiyar kauyen da suka yi awon gaba da masu garkuwa da mutane zuwa daji.“Kowa yana farin ciki a ƙauyen yanzu. An yi musayar wuta tsakanin sojoji da maharan kafin a ceto wadanda abin ya shafa.

“Sojoji sun yi kokari. Muna rokon Allah Ya ba su ikon ci gaba da gudanar da ayyukan alheri da suke yi.”

Source: The Nation

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp