Rikicin ya Barke Tsakanin Boko Haram da ISWAP, ‘Yan Ta’adda da Dama Sun Mutu

Rikicin ya Barke Tsakanin Boko Haram da ISWAP, ‘Yan Ta’adda da Dama Sun Mutu

 

Wani kazamin fada ya sake barkewa tsakanin bangaren Abubakar Shekau na Boko Haram da kungiyar IS a yammacin Afirka a ranar Alhamis din da ta gabata wanda ya kai ga kashe wani kwamanda da aka bayyana sunansa da “Kundu” da kuma mayakan da dama.

Fadan dai ya faru ne a tsakanin kananan hukumomin Dikwa da Bama.

Wata majiyar tsaro ta bayyana cewa, Kundu da tawagarsa suna aikin fashi ne a lokacin da ISWAP suka kama su a kan babura shida, kowannen su dauke da mayaka uku.

Zagazola Makama, wani mai sharhi kan harkokin tsaro da masu tada kayar baya a tafkin Chadi ya tabbatar da wannan fadan.

Ya ce, “An gwabza kazamin fada tsakanin ‘yan ta’addan wanda ya yi sanadin asarar rayuka da dama a bangaren ‘yan ta’addan na Boko Haram, yayin da ‘yan ta’addar ISWAP kadan suka samu raunuka.

“Yan ta’addar Boko Haram sun kai ga barin baburansu ga ‘yan ta’addar ISWAP.”

A wani labarin kuma, sojojin Najeriya sun kai farmaki a yankunan ISWAP a wasu hare-hare da suka kai inda suka kashe ‘yan ta’adda da dama ciki har da kwamandoji uku a yankin tafkin Chadi.

An samu labarin cewa jiragen yakin sojin kasar Super Tucano tare da hadin gwiwar rundunar sojin sama na Operation Hadin Kai sun lalata sansanoni uku a yankin arewacin jihar Borno.

An tattaro cewa an kaddamar da hare-haren da rundunar sojin sama ta Operation Hadin Kai ta shirya a maboyar ‘yan ta’addan a Rino, Jibularam da Kangarwa a kananan hukumomin Marte da Kukawa da sanyin safiyar ranar 14 ga watan Satumba.

Wani babban jami’in soji ya shaida wa wakilinmu cewa an kashe mayaka da dama a wasu hare-hare ta sama da aka kai a tafkin Chadi tsakanin Talata zuwa Alhamis.

Makama, wanda shi ma ya tabbatar da ayyukan, ya bayyana cewa, harin da aka kai ta sama ya yi barna na farko, ya auna maboyar ‘yan ta’addan da kuma sansanin horo a Rinu, inda ya kashe mayakan da ba a tantance adadinsu ba.

Majiyoyi sun ce ATF ta sake kai wani harin bam a Jibularam wanda ya yi sanadin kashe kwamandojin ISWAP uku da wasu mayaka da dama.

Wata majiya ta bayyana sunayen kwamandojin da Muhammed Balge, babban mai gabatar da kara; Malam Chiroma, wanda shi ne shugabansa na biyu; da kuma Amir Bashir, wanda aka fi sani da Iblis, wanda shi ne maharba kuma mai tada kayar baya.

“A wani aikin kuma, wanda ya biyo bayan sahihan bayanan sirri da rundunar soji ta Operation Hadin Kai ta samu, sojojin sun yi nasarar kashe ‘yan ta’adda da dama da ke tafiya cikin motoci biyu a cikin Kangarwa a karamar hukumar Kukawa.

“Lokacin da aka samu wannan kiran na tashin hankali, nan da nan jirgin NAF ya ruga zuwa wurin da suka kama tare da kashe ‘yan ta’adda da dama. Dakarun da aka girke a yankin ya nuna cewa ‘yan ta’addar sun yi mummunar barna sakamakon harin da jiragen suka kai,” inji majiyar sojan.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 32 minutes 42 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 14 minutes 7 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com