‘Yan Sanda sun Kama Mutumin da ya Damfari Ma’aikatan POS a Anambara

‘Yan Sanda sun Kama Mutumin da ya Damfari Ma’aikatan POS a Anambara

 

A jihar Anambra, ‘yan sanda sun kama wani mutum da ya damfari ma’aikatan POS

Rundunar ‘yan sandan jihar Anambra ta cafke wani mutum mai suna Chisom Nweke, mai shekaru 26, da ake zargi da yin amfani da laya wajen damfarar ma’aikatan POS a Awka da kewaye.

‘Yan sanda sun kama wanda ake zargin ne a ranar 15 ga watan Satumba da misalin karfe 9 na safe a Amawabia, karamar hukumar Awka ta Kudu a jihar Anambra.

Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, Ikenga Tochukwu ya fitar a ranar Alhamis, ta ce wanda ake zargin ya amsa laifinsa.

Ya ce binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa wadanda ake zargin sun yanke farar takarda mai girman kudi tare da ba wa ma’aikatan POS su ajiye.

Tochukwu ya ce ana ci gaba da kokarin cafke sauran ‘yan kungiyar sa.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 51 minutes 3 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 32 minutes 28 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com