Home Labarai Ambaliyar Ruwa ta Shafi Yara 75,000 a Najeriya da Niger

Ambaliyar Ruwa ta Shafi Yara 75,000 a Najeriya da Niger

Ambaliyar Ruwa ta Shafi Yara 75,000 a Najeriya da Niger

 

By Gaggawa Digest-Satumba 16, 2022

Kungiyar Save the Children International (SCI) ta ce kimanin kananan yara 75,000 ne ambaliyar ruwa ta shafa a Nijar da Najeriya a makonnin da suka gabata.

A cikin wata sanarwa a ranar Alhamis, ta ce sama da mutane 150,000 ne abin ya shafa ya bar al’umma da dama cikin rudani.

Sanarwar ta ce ambaliyar ta yi barna a yankunan Maradi, Zinder, Tillaberi da Tahoua na Nijar, da kuma jihohin Borno, Yobe, da Adamawa a Najeriya inda mutane sama da 100,000 suka shafa a Nijar kadai.

Shugabar kungiyar agaji ta Save the Children a Najeriya, Famari Barro, ta ce yana da matukar muhimmanci a samar da taimako ga mutanen da abin ya shafa musamman kananan yara, wadanda a kodayaushe suka fi shiga cikin mawuyacin hali.

Ya ce, “Yara na bukatar kwanciyar hankali, kuma muna bukatar mu tabbatar da cewa yara za su iya komawa makaranta a kwanaki masu zuwa. Yana da mahimmanci cewa akwai azuzuwa kuma amintacce ga yara kuma iyalai za su iya komawa gidajensu lafiya. ”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp