Home Labarai Ambaliyar Ruwa ta Shafi Yara 75,000 a Najeriya da Niger

Ambaliyar Ruwa ta Shafi Yara 75,000 a Najeriya da Niger

Ambaliyar Ruwa ta Shafi Yara 75,000 a Najeriya da Niger

 

By Gaggawa Digest-Satumba 16, 2022

Kungiyar Save the Children International (SCI) ta ce kimanin kananan yara 75,000 ne ambaliyar ruwa ta shafa a Nijar da Najeriya a makonnin da suka gabata.

A cikin wata sanarwa a ranar Alhamis, ta ce sama da mutane 150,000 ne abin ya shafa ya bar al’umma da dama cikin rudani.

Sanarwar ta ce ambaliyar ta yi barna a yankunan Maradi, Zinder, Tillaberi da Tahoua na Nijar, da kuma jihohin Borno, Yobe, da Adamawa a Najeriya inda mutane sama da 100,000 suka shafa a Nijar kadai.

Shugabar kungiyar agaji ta Save the Children a Najeriya, Famari Barro, ta ce yana da matukar muhimmanci a samar da taimako ga mutanen da abin ya shafa musamman kananan yara, wadanda a kodayaushe suka fi shiga cikin mawuyacin hali.

Ya ce, “Yara na bukatar kwanciyar hankali, kuma muna bukatar mu tabbatar da cewa yara za su iya komawa makaranta a kwanaki masu zuwa. Yana da mahimmanci cewa akwai azuzuwa kuma amintacce ga yara kuma iyalai za su iya komawa gidajensu lafiya. ”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp