Home Labarai Jihar Gombe ta Sanar da Bullar Cutar Kwalara, ta Kuma yi Sanadiyar...

Jihar Gombe ta Sanar da Bullar Cutar Kwalara, ta Kuma yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 10

Jihar Gombe ta Sanar da Bullar Cutar Kwalara, ta Kuma yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 10

 

AREWA AGENDA – A kalla mutane 10 ne suka mutu yayinda wasu 236 suka kamu da cutar kwalara a jihar Gombe.

Babban Sakataren Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko ta Jihar Gombe, Dakta Abdulrahman Shuaibu, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis yayin da yake zantawa da manema labarai a madadin Kwamishinan Lafiya, Dakta Habu Dahiru, kan bullar cutar a jihar.

Ya ce a ranar 20 ga Satumba, 2022, adadin wadanda suka kamu da cutar ya kai 236, inda ya ce a shekarar 2021, jihar ta samu adadin mutane 2,373 a cikin bullar cutar guda uku a shekarar da ta gabata.

“A wannan shekarar, daga ranar 30 ga watan Yuni, 2022, mun samu bullar cutar kwalara a karamar hukumar Balanga, kuma saboda shiri da gaggawar da aka yi, an shawo kan ta sosai ba tare da wani tashin hankali ba.

“Muna ganin yadda ruwan sama ya kara kamari, wanda ya haifar da ambaliya a sassan jihar da dama kuma hakan ya haifar da bullar cutar kwalara a Unguwani takwas da ke fadin kananan hukumomin Balanga, Yamaltu-Deba, Nafada, Funakaye da Gombe.

“Ma’aikatar Lafiya ta Jiha ta fara aiwatar da ayyukan kiwon lafiyar jama’a cikin gaggawa don rigakafi da shawo kan cutar kwalara. Ya zuwa jiya, 20 ga Satumba, 2022, an samu karuwar masu dauke da cutar a jihar Gombe, ya zuwa yanzu an jera masu kararraki 236.” Inji shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp