Gwamnatin Nijeriya Na Shirin Yiwa ASUU Kishiya

Ministan kwadago da samar da aikin yi na Najeriya, Chris Ngige ya damka takardar shaida ga kungiyar ma’aikatan koyarwa a jami’o’in Najeriya, wadda kungiya ce ta malaman jami’o’in tarayya da na jihohi.

Kungiyar mai suna CONUA a takaice ana ganin kai tsaye za ta kasance kishiya ga babbar kungiyar malaman jami’o’in Najeriya wato ASUU.

Wani jami’in gwamnatin Najeriya ya wallafa cewa an kafa kungiyar CONUA ne a shekara ta 2018 a jami’ar jihar Osun.

Kungiyar ASUU da gwamnatin Najeriya na kai ruwa rana saboda yajin aikin sai-baba-ta-gani da malaman jami’o’in suka shiga tsawon wata takwas ke nan yanzu, suna neman sai lallai gwamnati ta biya musu bukatunsu.

Duk da wani kokari da ban-baki da tattaunawa daga gwamnati sun kasa shawo kan kungiyar malaman kungiyar ASUU dakatar da yajin aiki.

Baya ga kungiyar CONUA, ministan kwadagon ya kuma amince da kungiyar likitoci masu koyarwa ta kasa (NAMDA)

an dai sami tirka-tirka tsakanin kungiyar malaman jami’ar ta ASUU da Gwamnatin tarayya Nijeriya, duk da cewa sun zauna zaman sulhu a tsakani amma ana kallon hakan yaci tura, ko da yake ana kallon samar da wannan kungiyar matsayin wani matashi na rage karfin kungiyar malaman ta ASUU.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 24 minutes 2 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 5 minutes 27 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com