Home Labarai Gwamnatin Jihar Zamfara ta Amince da Biyan Naira Dubu 30 Matsayin Mafi...

Gwamnatin Jihar Zamfara ta Amince da Biyan Naira Dubu 30 Matsayin Mafi Karancin Albashi

Gwamnatin jihar Zamfara ta amince ta aiwatar da mafi karancin albashin naira dubu 30 ga ma’aikatan jihar.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwar da babban daraktan yada labarai na ofishin mataimakin gwamna, Babangida Umar, ya fitar ranar Laraba a Gusau, babban birnin jihar, sanarwar tace mataimakin gwamna, Sanata Hassan Nasiha, ya sanar da hakan ne yayin karbar takardar yarjejeniyar da gwamnati ta kulla da ma’aikatan.

Mataimakin gwamnan ya nuna jin dadinsa game da yadda kungiyar kwadago ta nuna girma da fahimta yayin yarjejeniya da ma’aikatan gwamnati.

Fahimtarsu ta sa aka yanke shawarar aiwatar da mafi karancin albashi na N30,000 a watan Nuwamba.

“Halin da ake ciki na tabarbarewar tattalin arziki da kalubalen tsaro na cikin abubuwan da gwamnati ta yi la’akari da su kafin ta amince da aiwatar da sabon albashin,” in ji shi.

Ya kuma yaba wa kwamitin da Ambasada Bashir Yuguda ya jagoranta da ya wakilci gwamnati wajen cimma matsaya da kungiyoyin kwadago cikin lumana.

(NAN)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp