Home General Sojojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Hallaka Mayakan ISWAP 19 a Jihar Borno

Sojojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Hallaka Mayakan ISWAP 19 a Jihar Borno

Dakarun sojojin Nijeriya sun sami Nasarar hallaka mayakan boko haram tsagin ISWAP guda 19 tare da kame guda 73 a arewa maso gabashin kasar.

Wannan na kunshe ne ta ckin wata takardar sanarwa da aka rabawa manema labarai mai dauke da sa hannun darakatan yada labaran rundunar sojin Nijeriya Manjo Janar Musa Danmadami,dake dauke da kwanan watan 6 ga watan Oktoban 2022.

Sanarwar tace tsakanin 22 ga watan Satumba zuwa 4 ga watan Oktoban wannan shekara dakarun sojin Operation Hadin kai yayin da suke gudanar da ikin wazan da zaman lafiya a  kauyukan, tsunuka, da kuma biranen dake yakin arewa maso gabashin Nijeriya, dakarun sun gabatar da atisayen fatattakar mayakan a kananan hukumomin Biu, Damboa, kaga, Kukawa da Gubio duk a jihar Borno.

A yayin harin da dakarun sojojin suka kai sun sami nasara kame masu safarar kaya ga mayakan boko haram da na ISWAP, inda suka sami nasarar kwato kayayyaki da suka hadar da buhu 50 na busasshen Kifi, Buhu 2 na Busasshen Nama, sai kuma jarakuna 55 makare da man Fetir, buhu 1 na gwayi, sai buhu 13 na buredi, buhu wake guda 1, katan 5 na Omon wanke, 3 fakiti 3 na Batiri, sai jaka 50 ta maganin sauro, wayoyin salula 10, sai abun hawa guda 4, keke guda 1. Gami da zunzurutun kudi har naira miliyan 2 da dubu dari 479 da dari 740 da (2,479,740.00) gami da wasu kayyakin amfani.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp