Home General Sojojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Hallaka Mayakan ISWAP 19 a Jihar Borno

Sojojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Hallaka Mayakan ISWAP 19 a Jihar Borno

Dakarun sojojin Nijeriya sun sami Nasarar hallaka mayakan boko haram tsagin ISWAP guda 19 tare da kame guda 73 a arewa maso gabashin kasar.

Wannan na kunshe ne ta ckin wata takardar sanarwa da aka rabawa manema labarai mai dauke da sa hannun darakatan yada labaran rundunar sojin Nijeriya Manjo Janar Musa Danmadami,dake dauke da kwanan watan 6 ga watan Oktoban 2022.

Sanarwar tace tsakanin 22 ga watan Satumba zuwa 4 ga watan Oktoban wannan shekara dakarun sojin Operation Hadin kai yayin da suke gudanar da ikin wazan da zaman lafiya a  kauyukan, tsunuka, da kuma biranen dake yakin arewa maso gabashin Nijeriya, dakarun sun gabatar da atisayen fatattakar mayakan a kananan hukumomin Biu, Damboa, kaga, Kukawa da Gubio duk a jihar Borno.

A yayin harin da dakarun sojojin suka kai sun sami nasara kame masu safarar kaya ga mayakan boko haram da na ISWAP, inda suka sami nasarar kwato kayayyaki da suka hadar da buhu 50 na busasshen Kifi, Buhu 2 na Busasshen Nama, sai kuma jarakuna 55 makare da man Fetir, buhu 1 na gwayi, sai buhu 13 na buredi, buhu wake guda 1, katan 5 na Omon wanke, 3 fakiti 3 na Batiri, sai jaka 50 ta maganin sauro, wayoyin salula 10, sai abun hawa guda 4, keke guda 1. Gami da zunzurutun kudi har naira miliyan 2 da dubu dari 479 da dari 740 da (2,479,740.00) gami da wasu kayyakin amfani.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp