Home Labarai Dakarun Sojojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Kame Mai Bada Bayanan Sirri ga...

Dakarun Sojojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Kame Mai Bada Bayanan Sirri ga ISWAP a Jihar Borno

Dakarun sojojin Nijeriya sun sami nasarar kame wani dan Boko haram tsagin ISWAP daya kware a fannin kerawa da gyaran bindiga a kauyen Gorom dake karamar hukumar Monguno a jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata takardar sanarwa da shalkwatar rundunar ta aikewa PRNigeria mai dauke da sa hannun daraktan yada labaran rundunar sojin Nijeriya Manjo Janar Musa Danmadami,

Sanarwar tace a ranar 26 ga watan satumba zuwa 3 ga watan Oktoban wannan shekara dakarun sojojin sun sami nasara kame shi, dauke da gidan shirya alburushi guda 300 babu alburushin a ciki, wanda ake zargin yin amfanin dasu wajen shirya alburushin mai tsayin 7.62mm.

An dai zargi kwararren makerin bindigar ne da kasancewa guda cikin masu bada bayanan sirri ga mayakan Boko Haram tsagin ISWAP a wurare daban-daban, haka kuma rundunar ta sami nasarar cito ‘yan matan Chibok 2 da suka hadar da Yana Pogu da rejoice Senki wanda ke da lamaba ta 19 da 70 cikin jerin jadawalin ‘yan matan Chibok da aka sace da ‘ya’yan s a kauyen Bula Davo dake karamar hukumar Bama da kauyen Kawur dake Karamar Hukumar kunduga a jihar Borno gami da wasu wadanda aka sace su 12.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp