Home Labarai Dakarun Sojojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Kame Mai Bada Bayanan Sirri ga...

Dakarun Sojojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Kame Mai Bada Bayanan Sirri ga ISWAP a Jihar Borno

Dakarun sojojin Nijeriya sun sami nasarar kame wani dan Boko haram tsagin ISWAP daya kware a fannin kerawa da gyaran bindiga a kauyen Gorom dake karamar hukumar Monguno a jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata takardar sanarwa da shalkwatar rundunar ta aikewa PRNigeria mai dauke da sa hannun daraktan yada labaran rundunar sojin Nijeriya Manjo Janar Musa Danmadami,

Sanarwar tace a ranar 26 ga watan satumba zuwa 3 ga watan Oktoban wannan shekara dakarun sojojin sun sami nasara kame shi, dauke da gidan shirya alburushi guda 300 babu alburushin a ciki, wanda ake zargin yin amfanin dasu wajen shirya alburushin mai tsayin 7.62mm.

An dai zargi kwararren makerin bindigar ne da kasancewa guda cikin masu bada bayanan sirri ga mayakan Boko Haram tsagin ISWAP a wurare daban-daban, haka kuma rundunar ta sami nasarar cito ‘yan matan Chibok 2 da suka hadar da Yana Pogu da rejoice Senki wanda ke da lamaba ta 19 da 70 cikin jerin jadawalin ‘yan matan Chibok da aka sace da ‘ya’yan s a kauyen Bula Davo dake karamar hukumar Bama da kauyen Kawur dake Karamar Hukumar kunduga a jihar Borno gami da wasu wadanda aka sace su 12.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp