Home Labarai Dakarun Sojojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Kame Mai Bada Bayanan Sirri ga...

Dakarun Sojojin Nijeriya Sun Sami Nasarar Kame Mai Bada Bayanan Sirri ga ISWAP a Jihar Borno

Dakarun sojojin Nijeriya sun sami nasarar kame wani dan Boko haram tsagin ISWAP daya kware a fannin kerawa da gyaran bindiga a kauyen Gorom dake karamar hukumar Monguno a jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata takardar sanarwa da shalkwatar rundunar ta aikewa PRNigeria mai dauke da sa hannun daraktan yada labaran rundunar sojin Nijeriya Manjo Janar Musa Danmadami,

Sanarwar tace a ranar 26 ga watan satumba zuwa 3 ga watan Oktoban wannan shekara dakarun sojojin sun sami nasara kame shi, dauke da gidan shirya alburushi guda 300 babu alburushin a ciki, wanda ake zargin yin amfanin dasu wajen shirya alburushin mai tsayin 7.62mm.

An dai zargi kwararren makerin bindigar ne da kasancewa guda cikin masu bada bayanan sirri ga mayakan Boko Haram tsagin ISWAP a wurare daban-daban, haka kuma rundunar ta sami nasarar cito ‘yan matan Chibok 2 da suka hadar da Yana Pogu da rejoice Senki wanda ke da lamaba ta 19 da 70 cikin jerin jadawalin ‘yan matan Chibok da aka sace da ‘ya’yan s a kauyen Bula Davo dake karamar hukumar Bama da kauyen Kawur dake Karamar Hukumar kunduga a jihar Borno gami da wasu wadanda aka sace su 12.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp