Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Katsina ta Fatattaki ‘Yan Ta’addan tare da ceto Mutane 18 da aka yi Garkuwa da su

Rundunar ‘yan sandan jihar katsina tace ta sami nasarar fatattakar ‘yan bindiga a yayin da suka farwa kauyukan Baushe da Gatakawa dake karamar hukumar Kankara a jihar.

wannan na kushe ta cikin wata sanarwa da aka raba ga manema labarai da kakakin hukumar SP Gambo Isah ya fitar a madadin kwamishinan ‘yan sandan jihar.

sanarwar tace ‘yan ta’addan masu tarin yawa bisa babura dauke da bindigu kirar AK 47, sun tasamma kauyukan inda suke harbi kan mai uwa da wabi, nan jami’an ‘yan sanda suka kai dauki bayan samun rahotanni bisa jagograncin baturen ‘yan sanda na kankara.

rundunar ta yi nasarar fatattakar ‘yan ta’addan daga kokaringudanar da mummunan harin da suka yi niya tare da kubutar da dukkannin wadanda aka yi garkuwa da su. inda  suka sami nasarar kwato babura biyar da shanu biyu.

sai dai sanarwa ta bayyana ewa ‘yan bindigar sun halaka mutum biyu mazauna kauyen baya ga raunata mutum guda. ko da yake ana kallon an hallaka ‘yan bindigar da dama kko kuma sun tsere da raunikan harbi a jikkunansu.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 19 minutes 55 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 1 minute 20 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com