Home Labarai Ma’aikatan Jinya na Gaggawa Sun yi Alkawarin Bada, Magunguna Kyauta ga Membobin...

Ma’aikatan Jinya na Gaggawa Sun yi Alkawarin Bada, Magunguna Kyauta ga Membobin NURTW a Kwara

Daga Fatima Mohammed-Lawal

Kungiyar ma’aikatan jinya ta gaggawa wato Emergency Nurses Assoiation of Nigeria (ENAN) reshen jihar Kwara ta yi alkwarin duba lafiya gami da bada magunguna kyauta ga mambobin kungiyar sufuri ta (NURTW), ta jihar.

Kamfanin dillanci labarai na Nijeriya NAN ya ruwaito cewa wannan na wani bangare na bikin makon ma’aikatan gaggawa na duniya na shekarar 2022, wanda aka yiwa take “ standing strong”

Ayyukan kiwon lafiya sun hadar da duba marasa lafiya kyauta gami da bada magani kyauta, sai kuma gwajin shan miyagun kwayoyi, dakuma bada gajin gaggawa ga mambobin kungiyar da hadari ya rutsa dasu.

Da take jawabi a yayin taron bikin shugabar kungiyar Mrs Bashirat Dere, tace an ware ranar ne domin yin murna da irin gudunmawar da ma’aikatan jinyar ke bayarwa ga Al’umma, hadi da bayyana irin kalubalen da suke fuskanta da kuma walwalar su.

Dere ta bayyana bangare likitocin Jinya na gaggawa fannin ne na kwararru a cikin likitocin jinya, wanda ke mayar da hankali a bangare lura da marasa lafiya da ke bukatar kulawar ta musamman domin tserartar dasu daga mutuwa.

A cewar ta, ma’aikatan jinya na gaggawa suna lura da marasa lafiya da ke fama da rauni ko kuma yanayin rashin  lafiya mai tsananni wadda ke bukatar kulawar gaggawa.

Masaniyar ta tabbatar da cewa tun da wadannan kwararrun suna aiki a cikin yanayi na rikici, dole ne su iya hanzarta gano hanya mafi kyau don ura da marasa lafiya da kuma rage musu zugi.

Ta kuma bukaci mahukunta a kowanne mataki dasu lura da walwala da jin dadin mambobin wannan kungiya.

Da yake jawabi Babban Daraktan asibitin koyarwa na jami’ar Ilorin (UITH), Farfesa Abdullahi Dasilva, yay aba da kwazon aiki da sadaukarwar ma’aikatan jinyar na gaggawa wajen ceto rayukan Al’umma.

Ya kuma bukace su dasu tsaya kai da fata wajen gudanar da ayyukan su, wajen  ceto rayukan Al’umma.

Dasilva ya kuma yi alkawarin cewa cibiyar lura da lafiya ta manyan makarantu za ta ci gaba da talafawa mambobin ta hanyar horarwa da sake horardama’aikatan ta.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp