Home General Rundunar ‘yan sanda Nijeriya  zata Girke Jami’anta a Kan haryar jirgin kasan...

Rundunar ‘yan sanda Nijeriya  zata Girke Jami’anta a Kan haryar jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna

Za’a girke Jami’an ‘yan sanda, biyo bayan dawo da jigilar fasinjoji a jirgin kasa daga Abuja zuwa kaduna.
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan na kasa CSP Olumuyiwa Adejobi, mnipr, mipra ya fitar a birnin tarayyar kasar Abuja mai dauke da kwanan watan 4 ga watan Disamba 2022 da aka akewa PRNigeria.
Sanarwar tace babban sefeton ‘Yan sanda Nijeriya Usman Alkali Baba, psc(+), NPM, NEAPS, fdc, CFR, ya bada umarnin girki Jami’an kwantar da tarzoma na Mobile Force, K-9, Force na kwarru da kuma Jami’an ‘yan sandan layin dogo domin gudanar da ayyukan tsaro kan hanyar jirgin kasan daga Abuja zuwa Kaduna ranar litinin 5 ga Disambar 2022.
Inda sanarwa ta kara da cewa Rundunar ‘yan sandan Nijeriya na cigaba da tattaunawa da hukumar dake lura da Jiragen Kasan Nijeriya da sauran Jami’an tsaro domin gudanar da aikin tsaron Al’umma yadda ya kamata.
Dakarun zasu lura da muhimman wuraren na tashar jirgin kasar da hanyar da yake bi da kuma bada shawarwari don samar da ingantacce tsaro ga fasinjoji da dukiyoyin su ta hanyar kare su ga dukkan abinda kaje kazo
Babban Sifeton ‘yan sanda ya kuma tabbarwa da Al’umma kasar musamman fasinjojin jirgin kasar cewa zasu kare su da lafiyar su da dukiyar su da zarar sun hau kan hanya domin yin balaguro, dama sauran fasinjojun dake kan jirgin kasa a dukkan fadin kasar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp