Home General Sojojin Nijeriya sun Kama Wanda ya hallaka Ahmamad Gulak

Sojojin Nijeriya sun Kama Wanda ya hallaka Ahmamad Gulak

Dakarun rundunar sojojin Nijeriya sun kama mataimakain kwamandan mayakan kungiyar ‘yan awaren Biyafara IPOB Nwagwu Chiwendu, wanda ke hannun bisa kisan dan siyasar yankin Arewacin kasar Ahmed Gulak.
PRNigeria ta tattaro cewa Chiwendu shine mai horas da dakarun kungiyar sarrafa makamai, wanda ke matsayin na biyu cikin masu fada aji a tawagar, wanda kuma shine shugaban kungyar a jihar Imo.
Hamshakin dan Ta’addan ya bar aikin cikin rundunar soji Nijeriya, inda ya koma cikin kungiyar ta IPOB tun watan janairun 21.
“yayin aiki a cikin rundunar Operation hadin kai (OPHK) yana kuma cikin wanda suka sami horo, an kama shi jiya yayin bikin binne mahaifinsa a Mbaise. Ya kuma kai mu zuwa sansanin sun a Obowo da daddare.
“ya amsa cewa shine ya hallaka Gulak, ya kuma tabbatar da cewa sansanin ke da alhakin yin garkuwa da matafiya 2 akan hanyar Owerri zuwa Okigwe inda suka hallaka sifeton ‘yan sanda guda biyu dake musu rakiya.
haka kuma suke majiyar ta bayyanawa PRNigeria cewa, “sun eke da alhakin hallaka sojoji a wannan yanki tare ga kone motarsu kirar Hilux makon daya gabata. Haka kuma sun bada gudunmawa wajen kai hari ofishin hukumar zabe mai zaman kanta na INEC dake Owerri. Hanzu haka dai yana hannun jami’an ‘yan sanda.
By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp