Sojojin Nijeriya sun Kama Wanda ya hallaka Ahmamad Gulak

Dakarun rundunar sojojin Nijeriya sun kama mataimakain kwamandan mayakan kungiyar ‘yan awaren Biyafara IPOB Nwagwu Chiwendu, wanda ke hannun bisa kisan dan siyasar yankin Arewacin kasar Ahmed Gulak.
PRNigeria ta tattaro cewa Chiwendu shine mai horas da dakarun kungiyar sarrafa makamai, wanda ke matsayin na biyu cikin masu fada aji a tawagar, wanda kuma shine shugaban kungyar a jihar Imo.
Hamshakin dan Ta’addan ya bar aikin cikin rundunar soji Nijeriya, inda ya koma cikin kungiyar ta IPOB tun watan janairun 21.
“yayin aiki a cikin rundunar Operation hadin kai (OPHK) yana kuma cikin wanda suka sami horo, an kama shi jiya yayin bikin binne mahaifinsa a Mbaise. Ya kuma kai mu zuwa sansanin sun a Obowo da daddare.
“ya amsa cewa shine ya hallaka Gulak, ya kuma tabbatar da cewa sansanin ke da alhakin yin garkuwa da matafiya 2 akan hanyar Owerri zuwa Okigwe inda suka hallaka sifeton ‘yan sanda guda biyu dake musu rakiya.
haka kuma suke majiyar ta bayyanawa PRNigeria cewa, “sun eke da alhakin hallaka sojoji a wannan yanki tare ga kone motarsu kirar Hilux makon daya gabata. Haka kuma sun bada gudunmawa wajen kai hari ofishin hukumar zabe mai zaman kanta na INEC dake Owerri. Hanzu haka dai yana hannun jami’an ‘yan sanda.
By PRNigeria

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 37 minutes 46 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 19 minutes 11 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com