‘Yan bindiga sun hallaka jami’an tsaron sa kai 6 a jihar Kaduna

Rahotannin daga jihar Kaduna na bayyana cewa wasu ‘yan bindiga sun hallaka jami’an tsaron sa kai na bijilanti 6 a shingen binciken ababawan hawa na Awaro dake yammacin birnin-Gwari, a karamar hukumar birnin Gwari ta jihar Kaduna dake arewa maso yammacin Nijeria.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 4 na yammacin ranar laraba.
Guda cikin Jami’an bijilantin Usman Babangida, ya tabbatarwa da maneman labarai mutuwar abokan aikin nasa a ranar laraba sakamakon harin ‘yan bindiga a shingen binciken Ababan hawa da suke gudanar da ayyukan su.
Inda yace ‘yan bindigar sun fara harfi kan mai uwa da wabi bayan sun hangi jami’an na bijilanti, in da suka hallaka 6 daga cikin su, ya kuma ce wadanda aka hallaka din anyi jana’idar su kamar yadda addinin musulunci yayi tanadi.
Yace lamarin ya faru ne jim kadan bayan da ‘yan bindiag suka yi wani artabu da wasu ‘yan bindiga a wani kauye dake kusa da sum ai suna Bugai.
Ko da PRNigeria ta tuntubi kakakin rundunar ‘yan sanda jihar Kaduna Muhammad Jalige ta wayar tarho bata same shi ba.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 18 minutes 27 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 59 minutes 52 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com