Home Labarai NAPTIP ta kuɓutar da mata 11 da aka yi niyyar safararsu zuwa...

NAPTIP ta kuɓutar da mata 11 da aka yi niyyar safararsu zuwa Libya

Hukumar yaƙi da fataucin bil-Adama a Najeriya NAPTIP ta ce tana gudanar da bincike kan lamarin da ya kai ga safarar wasu mata ‘yan Najeriya 11 daga ƙasar.

An ceto ‘yan matan ne a makwaɓciyar ƙasar Jamhuriyar Nijar lokacin da wata ƙungiyar masu safarar mutane ke niyyar jigilar su zuwa ƙasar Libya.

Ƴan matan da suka kasance dukkaninsu matasa, an dawo da su gida Najeriya tare da miƙa su ga hukumar hana fataucin mutane ta kasa NAPTIP reshen Sokoto.

Kwamandan NAPTIP na shiyyar Sokoto, Abubakar Tabra ya shaida wa BBC cewa jami’an hukumar kula da shige da fice ta ƙasa reshen Illela ne suka karɓi ‘yan matan a karshen makon da ya gabata, inda ya ce a yanzu sun soma bincike da nufin kamo waɗanda ake zargi da safarar ƴan matan.

Ya kuma ce ana kuma kokarin bincike don gano ‘yan uwan ƴan matan don sake haɗa su da iyalansu.

Bayanan da aka tattara sun nuna cewa waɗanda abin ya rutsa da su sun fito ne daga kudancin Najeriya.

Rahotanni sun ce an sace musu wayoyinsu da kayayyakinsu a cikin dazukan Jamhuriyar Nijar, inda waɗanda suka yi safararsu suka yi watsi da su, kafin jami’an ‘yan sandan Nijar ɗin su kuɓutar da su tare da miƙa su ga jami’an shige da fice na Najeriya da ke kan iyaka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp