INEC ta saka ranar bada satifiket ga zababbun Gwamnonin Nijeriya

Hukumar zaɓe mai zaman kanta a Najeriya ta ce ta saka ranakun da za ta bayar da takardar shaidar cin zaɓe ga zaɓaɓɓun gwamnoni a jihohin ƙasar da aka gudanar da zaɓen gwamna.

A wata sanarwar da hukumar INEC din ta fitar mai ɗauke da sa- hannun shugaban kwamitin yada labarai da ilimantar da masu kada ƙuri’a na hukumar Festu Okoye, ta ce sashe na 72 (1) na dokar zaɓen ƙasar ta 2022, ya ɗora wa hukumar alhakin bayar da takardar shaidar cin zaɓe ga zaɓaɓɓun ‘yan takara a cikin kwana 14 da yin zaɓen.

A kan haka ne hukumar ta ce ta saka ranar Laraba 29 ga watan Maris da kuma 31 ga watan na Maris a matsayin ranar da za ta bayar da takardar shaidar cin zaɓen ga zaɓaɓɓun gwamnoni da mataimakansu, tare kuma ‘yan majalisun dokokin jihohi.

Sanarwar ta ce za a bayar da takardar shaidar cin zaɓen ne a harabar ofisoshin hukumar da ke faɗin jihohin ƙasar.

Hukumar zaɓen ta ce kwamishinonin INEC na jihohi da ma’aikatan hukumar za su sanar da zaɓaɓɓun takamammiyar ranar da za su karɓi takardun shaidar.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 41 minutes 52 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 23 minutes 17 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com