Home DUNIYA Sama da yara dubu 500 na fama da tsananin yunwa a Yemen-UNICEF

Sama da yara dubu 500 na fama da tsananin yunwa a Yemen-UNICEF

Asususn tallafa wa kananan yara na majalisar dinkin duniya UNICEF yace akalla yara dubu 540 ne ke fama da matsanaciyar yunwa a Yemen, da rashin abinci mai gina jiki, wanda kuma ke barzana ga lafiyar su.

A cikin wani kundin bayani da asusun ya fitar, ya ce wannan matsala na kashe yaro guda cikin kowanne minti 10, a kasar da ke fama da tashin hankali.

Asusun na UNICEF ya kuma ci gaba da cewa bayan wadannan yara, akwai wasu guda miliyan 11 da ke neman tallafin gaggawa a kasar ta Yemen, inda kuma ake bukatar dala miliyan 488 a shekarar nan kadai don tallafa wa yaran.

Yakin da ake ci gaba da gwabzawa a kasar na ci gaba da taka rawa wajen jefa yaran cikin tashin hankali, tare da hana ma’aikatan jinkai shiga wasu yankunan don kai musu kayan tallafi, a cewar UNICEF.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp