Home DUNIYA Sama da yara dubu 500 na fama da tsananin yunwa a Yemen-UNICEF

Sama da yara dubu 500 na fama da tsananin yunwa a Yemen-UNICEF

Asususn tallafa wa kananan yara na majalisar dinkin duniya UNICEF yace akalla yara dubu 540 ne ke fama da matsanaciyar yunwa a Yemen, da rashin abinci mai gina jiki, wanda kuma ke barzana ga lafiyar su.

A cikin wani kundin bayani da asusun ya fitar, ya ce wannan matsala na kashe yaro guda cikin kowanne minti 10, a kasar da ke fama da tashin hankali.

Asusun na UNICEF ya kuma ci gaba da cewa bayan wadannan yara, akwai wasu guda miliyan 11 da ke neman tallafin gaggawa a kasar ta Yemen, inda kuma ake bukatar dala miliyan 488 a shekarar nan kadai don tallafa wa yaran.

Yakin da ake ci gaba da gwabzawa a kasar na ci gaba da taka rawa wajen jefa yaran cikin tashin hankali, tare da hana ma’aikatan jinkai shiga wasu yankunan don kai musu kayan tallafi, a cewar UNICEF.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp