Home Labarai APC, PDP sun kalubalanci DSS ta kama masu neman dakile rantsar da...

APC, PDP sun kalubalanci DSS ta kama masu neman dakile rantsar da Asiwaju

A Najeriya, majalisun yakin neman zabe na jam’iyyar APC da na PDP sun kalubalanci  hukumar tsaro ta DSS ta yi wa wadanda suke kitsa munakisar samar da gwamnatin rikon kwarya a kasar dirar mikiya.

A mabanbantan ganawa da suka yi da wata jaridar kasar a ranar Laraba a Abuja, sun ce neman samar da gwamnatin rikon kwarya abu ne da ya saba wa doka, saboda haka kamata ya yi a kama duk Wanda yake da hannu a lamarin.

Sun bayyana haka ne biyo bayan sanarwar da huukumar tsaron DSS din ta fitar, wadda ke cewa wasu mutane na kulla munaakisar samar da gwamnatin rikon kwarya a Najeriya.

Tun da farko hukumar DSS ta fada a wata sanarwa da ta samu sa hannun kakakinta Peter Afunanya cewa wasu ‘yan siyasa a Najeriya na kokarin dakile rantsar da zababben shugaban kasar, Bola Ahmed Tinubu a ranar  29 ga watan Mayu mai zuwa.

Dan takarar APC ne dai ya lashe zaben shugaban kasa da aka yi a ranar 25 ga watan Fabrairu da kuri’u 8,794,726 inda ya doke abokin hamayyarsa na PDP, Atiku Abubakar, wanda ya samu  kuri’u 6,984,520 da Peter Obi  na jam’iyyar Labour mai kuri’u 6,101,533.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp