Home DUNIYA Mata masu juna biyu sama da 80,000 ke mutuwa duk shekara a...

Mata masu juna biyu sama da 80,000 ke mutuwa duk shekara a Najeriya – UNICEF

Wannan na zuwa ne, yayin da hukumomin lafiya na duniya ke ci gaba da jan hankalin kasashe, musamman masu tasowa muhimmancin inganta shirin kula da lafiyar mata masu juna biyu.

Majalisar Duniya ta ce rayuwar mata masu juna biyu, ko kuma yayin haihuwa na cikin matukar hadarin gaske a nahiyar Afirka, don haka ana bukatar samar da wani shiri na musamman da zai magance wannan matsala.

A cewar UNICEF, mata 225 ne ke mutuwa a kowace rana a Najeriya, sakamakon mace-macen mata masu juna biyu ko kuma yayin haihuwa, inda suke neman hukumomi su dauki matakin gaggawa don dakile wannan matsala.

Masana kiwon lafiya na danganta mace-macen mata masu juna biyu ko kuma yayin haihuwa na da nasaba ne da sakaci zuwa duba lafiyarsu a lokacin da ya dace, yayin da wasu kuma ke fama da rashin cibiyoyin kula da lafiya a yankunan su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp