Home Labarai APC, PDP sun kalubalanci DSS ta kama masu neman dakile rantsar da...

APC, PDP sun kalubalanci DSS ta kama masu neman dakile rantsar da Asiwaju

A Najeriya, majalisun yakin neman zabe na jam’iyyar APC da na PDP sun kalubalanci  hukumar tsaro ta DSS ta yi wa wadanda suke kitsa munakisar samar da gwamnatin rikon kwarya a kasar dirar mikiya.

A mabanbantan ganawa da suka yi da wata jaridar kasar a ranar Laraba a Abuja, sun ce neman samar da gwamnatin rikon kwarya abu ne da ya saba wa doka, saboda haka kamata ya yi a kama duk Wanda yake da hannu a lamarin.

Sun bayyana haka ne biyo bayan sanarwar da huukumar tsaron DSS din ta fitar, wadda ke cewa wasu mutane na kulla munaakisar samar da gwamnatin rikon kwarya a Najeriya.

Tun da farko hukumar DSS ta fada a wata sanarwa da ta samu sa hannun kakakinta Peter Afunanya cewa wasu ‘yan siyasa a Najeriya na kokarin dakile rantsar da zababben shugaban kasar, Bola Ahmed Tinubu a ranar  29 ga watan Mayu mai zuwa.

Dan takarar APC ne dai ya lashe zaben shugaban kasa da aka yi a ranar 25 ga watan Fabrairu da kuri’u 8,794,726 inda ya doke abokin hamayyarsa na PDP, Atiku Abubakar, wanda ya samu  kuri’u 6,984,520 da Peter Obi  na jam’iyyar Labour mai kuri’u 6,101,533.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp