Home Labarai APC, PDP sun kalubalanci DSS ta kama masu neman dakile rantsar da...

APC, PDP sun kalubalanci DSS ta kama masu neman dakile rantsar da Asiwaju

A Najeriya, majalisun yakin neman zabe na jam’iyyar APC da na PDP sun kalubalanci  hukumar tsaro ta DSS ta yi wa wadanda suke kitsa munakisar samar da gwamnatin rikon kwarya a kasar dirar mikiya.

A mabanbantan ganawa da suka yi da wata jaridar kasar a ranar Laraba a Abuja, sun ce neman samar da gwamnatin rikon kwarya abu ne da ya saba wa doka, saboda haka kamata ya yi a kama duk Wanda yake da hannu a lamarin.

Sun bayyana haka ne biyo bayan sanarwar da huukumar tsaron DSS din ta fitar, wadda ke cewa wasu mutane na kulla munaakisar samar da gwamnatin rikon kwarya a Najeriya.

Tun da farko hukumar DSS ta fada a wata sanarwa da ta samu sa hannun kakakinta Peter Afunanya cewa wasu ‘yan siyasa a Najeriya na kokarin dakile rantsar da zababben shugaban kasar, Bola Ahmed Tinubu a ranar  29 ga watan Mayu mai zuwa.

Dan takarar APC ne dai ya lashe zaben shugaban kasa da aka yi a ranar 25 ga watan Fabrairu da kuri’u 8,794,726 inda ya doke abokin hamayyarsa na PDP, Atiku Abubakar, wanda ya samu  kuri’u 6,984,520 da Peter Obi  na jam’iyyar Labour mai kuri’u 6,101,533.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp