Home Labarai ‘Yan bindiga sun kashe mutum 34 a sansanin ‘yan gudun hijira da...

‘Yan bindiga sun kashe mutum 34 a sansanin ‘yan gudun hijira da ke Benue

Rahotanni na bayyana cewa ‘Yan bindiga sun hallaka mutane 34 a wani hari da suka kai sansanin ‘yan gudun hijira da ke wata makarantar firamari a ƙauyen Mgaban da ke Ƙaramar Hukumar Benue ta Arewa a ranar Juma’a da daddare.

Wani mazaunin yankin ya shaidawa manema labarai cewa maharan sun isa ƙauyen ne da misalin ƙarfe 9 na daren Juma’a.

Ya ce cikin waɗanda aka kashe akwai wata mata mai ciki da ɗanta sannan kuma da dama sun jikkata.

Ka zalika mai bayar da shawara kan harkokin tsaro na Ƙaramar Hukumar Guma Christopher Waku, ya shaida wa jaridar cewa an kashe mutum 34 yayin da aka jikkata wasu 40 na daban.

Kakakin ‘yan sanda ta jihar SP Catherine Anene, ta tabbatar da faruwar lamarin ta hanyar sakon waya da ta turawa wakilin jiridar, sai dai ba ta yi wani cikakken ƙarin bayani ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp