NiMet ta yi gargaɗi kan samun ruwan sama mai karfi a arewacin Najeriya

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargadin samun ruwan sama mai karfin gaske gami da tsawa a wasu sassa na arewa maso gabashin Najeriya.

Kakakin hukumar, Muntari Ibrahim ne ya bayyana haka ta cikin wata sanarwa da ya fitar.

A cewarsa, jihohin da za su fuskanci wannan yanayi sun hada da Borno da Adamawa da Gombe da kuma Taraba.

Sannan sanarwar ta kuma ce za a samu ruwa tafe da iska a jihohi irinsu Gombe da Bauchi da Benue da Filato da Nasarawa da Enugu da Ebonyi.

Sai wasu kuma jihohin kudanci. Rahoton ya ce za a shafe tsawon sa’a uku zuwa shida ana tafka ruwan.

Nimet ta shawarci mutane suyi takatsan-tsan da kasancewa masu kula saboda tsaronsu.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 9 minutes 32 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 50 minutes 57 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com