Home Labarai NiMet ta yi gargaɗi kan samun ruwan sama mai karfi a arewacin...

NiMet ta yi gargaɗi kan samun ruwan sama mai karfi a arewacin Najeriya

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargadin samun ruwan sama mai karfin gaske gami da tsawa a wasu sassa na arewa maso gabashin Najeriya.

Kakakin hukumar, Muntari Ibrahim ne ya bayyana haka ta cikin wata sanarwa da ya fitar.

A cewarsa, jihohin da za su fuskanci wannan yanayi sun hada da Borno da Adamawa da Gombe da kuma Taraba.

Sannan sanarwar ta kuma ce za a samu ruwa tafe da iska a jihohi irinsu Gombe da Bauchi da Benue da Filato da Nasarawa da Enugu da Ebonyi.

Sai wasu kuma jihohin kudanci. Rahoton ya ce za a shafe tsawon sa’a uku zuwa shida ana tafka ruwan.

Nimet ta shawarci mutane suyi takatsan-tsan da kasancewa masu kula saboda tsaronsu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp