Home Labarai Sama da mutane 100 sun mutu cikin sa’o’i 48 a hare-haren jihar...

Sama da mutane 100 sun mutu cikin sa’o’i 48 a hare-haren jihar Plateau

Wasu bayanai na nuna cewa cikin sa’o’I 48 hare-haren ‘yan ta’adda ya hallaka mutanen da yawansu ya haura 100 a wasu sassa na jihar Pilato dai dai lokacin da gwamnatin jihar ta sanya dokar takaita walwalar jama’a a yankunan da hare-haren ke faruwa.

Dan Majalisar tarayya da ke wakiltar Mangu da Bokkos Solomon Maren yayin jawabinsa gaban zaman zauren majalisar ranar laraba, ya ce mahara na ci gaba da kai hare-hare kan kauyuka tare da kisan mutanen da basu ji ba basu gani ba.

Mr Maren, ya bayyana cewa hare-haren sun fi tsananta a yankin da ya ke wakilta a jihar ta Pulato da ke tsakiyar Najeriya wanda ke nuna bukatar daukar mataki lura da yadda mutanen kauyukan da ake kai hare-haren ke rayuwa cike da fargaba.

Dan Majalisar ya bayyana cewa cikin sa’o’I 48 sai da hare-haren ya kashe mutane fiye da 100 wanda ke nuna mutuwar mutanen da yawansu yah aura 200 a makamantan hare-haren cikin watanni 2 da suka gabata.

A cewar Mr Maren maharan na kone gidaje da gonaki har ma da shagunan da ake adana amfanin gona yana mai kakkausar suka ga matakan da gwamnati ke dauka a kokarin yaki da matsalar tsaron da yankuna da dama ke fama da shi a Najeriya.

Matsalar tsaro na ci gaba da ta’azzara a sassan Najeriya musamman yankin arewaci inda ‘yan bindiga ke kai hare-haren ba gaira babu dalili tare da kisan tarin mutane da kuma sace dukiyoyinsu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp