Home DUNIYA Yankin Sahel na bukatar kudaden yaki da masu tsattsauran ra’ayi- MDD

Yankin Sahel na bukatar kudaden yaki da masu tsattsauran ra’ayi- MDD

Babbar jami’ar Majalisar Dinkin Duniya da ke kula da nahiyar Afrika Martha Pobee, ta koka da yadda yankin Sahel ke matsayin matattarar ayyukan ta’addanci sakamakon yadda ake ganin karuwar tashe-tashen hankula da ke da nasaba da masu tsattsauran ra’ayin addini bayan gazawar rundunar hadin gwiwa wajen yakar kungiyoyin ‘yan ta’adda da ya ta’azzara rashin tsaro a yankin.

Martha wadda ita ce mataimakiyar babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya da ke kula da nahiyar Afrika, ta bayyana hakan ne a lokacin taron majalisar tsaro, wanda ya tattauna kan yadda za a yaki kungiyoyin ta’addanci da ke da alaka da kungiyar IS da al-Qaida.

A shekarar 2014 ne aka samar da rundunar hadin gwiwa tsakanin kasashen Burkina Faso da Chadi da Mauritania da kuma Nijar, ganin cewa a shekarar da ta gabata Mali ta fice daga cikin wannan tafiya.

Sai dai a cewar Pobee tun a watan Janairun da ya gabata, rabon da rundunar ta gudanar da wani gagarumin aiki, saboda kintsawa don tunkarar sabbin kalubalen da ke gaban ta, wanda ke da nasaba da rashin kudaden tafiyar da harkokinta kama daga yaki da ‘yan ta’addan kai tsaye da kuma rage tsaurin akida tsakanin jama’ar yankin.

A baya-bayan nan ne Burkina Faso da kuma jamhuriyar Nijar, suka sake inganta alakar su da Mali, don tunkarar kalubalen tsaro a iyakokin kasashen su.

Jami’ar ta yi gargadin cewar rashin cimma wata jituwa tsakanin kasashen waje abokan huldar su ne ya sanya rundunar ta gaza samun gudunmuwar kudi don gudanar da ayyukan ta yadda ya kamata.

Toh sai dai shugaban kungiyar kasashen G5 Sahel Eric Tiare, ya ce an kammala tsara sabbin shirye-shiryen yadda rundunar za ta rinka gudanar da aikin ta, wanda za a mikawa majalisar tsaro da kuma kungiyar tarayyar Afrika don amincewa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp