Home Labarai Sama da mutane 100 sun mutu cikin sa’o’i 48 a hare-haren jihar...

Sama da mutane 100 sun mutu cikin sa’o’i 48 a hare-haren jihar Plateau

Wasu bayanai na nuna cewa cikin sa’o’I 48 hare-haren ‘yan ta’adda ya hallaka mutanen da yawansu ya haura 100 a wasu sassa na jihar Pilato dai dai lokacin da gwamnatin jihar ta sanya dokar takaita walwalar jama’a a yankunan da hare-haren ke faruwa.

Dan Majalisar tarayya da ke wakiltar Mangu da Bokkos Solomon Maren yayin jawabinsa gaban zaman zauren majalisar ranar laraba, ya ce mahara na ci gaba da kai hare-hare kan kauyuka tare da kisan mutanen da basu ji ba basu gani ba.

Mr Maren, ya bayyana cewa hare-haren sun fi tsananta a yankin da ya ke wakilta a jihar ta Pulato da ke tsakiyar Najeriya wanda ke nuna bukatar daukar mataki lura da yadda mutanen kauyukan da ake kai hare-haren ke rayuwa cike da fargaba.

Dan Majalisar ya bayyana cewa cikin sa’o’I 48 sai da hare-haren ya kashe mutane fiye da 100 wanda ke nuna mutuwar mutanen da yawansu yah aura 200 a makamantan hare-haren cikin watanni 2 da suka gabata.

A cewar Mr Maren maharan na kone gidaje da gonaki har ma da shagunan da ake adana amfanin gona yana mai kakkausar suka ga matakan da gwamnati ke dauka a kokarin yaki da matsalar tsaron da yankuna da dama ke fama da shi a Najeriya.

Matsalar tsaro na ci gaba da ta’azzara a sassan Najeriya musamman yankin arewaci inda ‘yan bindiga ke kai hare-haren ba gaira babu dalili tare da kisan tarin mutane da kuma sace dukiyoyinsu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp