Home Labarai Najeriya ta sake komawa ta ɗaya wajen fitar da ɗanyen mai a...

Najeriya ta sake komawa ta ɗaya wajen fitar da ɗanyen mai a Afirka

Najeriya ta sake komawa matsayinta ta ɗaya a cikin jerin ƙasashe masu fitar da ɗanyen mai bayan da ta samu ƙari a yawan ɗanyen man da take fitarwa a kowace rana.

A watan Mayu, alƙaluma sun sun nuna cewa Najeriya ta rinƙa fitar da ɗanyen mai ganga miliyan 1.184.

Alƙaluman wata-wata da Ƙungiyar Ƙasashe Masu Fitar da Man Fetur da Duniya (OPEC) ta fitar sun nuna cewa Najeriya ta ɗara Libya, mai fitar da ganga miliyan 1,158, da Angola mai fitar da ganga miliyan 1,111, da kuma Algeria mai fitar da ganga 962,000.

A cikin shekarar nan ta 2023 ne dai yawan ɗanyen man da Najeriya ke fitarwa zuwa ƙasashen ƙetare ya ragu matuƙa, inda ya koma ganga 999,000 a kowace rana, lamarin da ya mayar da ita bayan ƙasashen Libya da Angola da Algeria.

Najeriya dai na fama da matsalar masu satar ɗanyen mai, da rashin tsaro a yankin Neja-Delta mai arziƙin man fetur, da fasa bututan mai, waɗanda gwamnati ta ce su ne manyan dalilan da suka sanya fitar da ɗanyen man ya yi ƙasa sosai.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp