Gwamnatin jihar Kano ta gaggauta magance ayyukan daba a jihar – Majalisa

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta yi Kira ga Gwamnatin Jihar Kano data Umarci Kwamishinan ‘Yan sanda na Jihar da sauran hukumomin tsaro dasu Kai daukin gaggawa Unguwannin dake cikin Dala dake fuskantar matsalolin ‘Yan daba da masu kwace dake damun Yankin tsawon kwanaki.

Kiran ya biyo bayan kudurin da Shugaban Masu Rinjaye na majalisar Kuma wakilin Dala Hon Lawan Hussaini ya gabatar a zauren majalisar inda ya ce tsawon kwanaki batagari sun addabi Unguwannin na Dala da adakawa da kewaye da kwace da sare sare da tashin hankali kala kala a tsakar dare.

A cewar sa lamarin ya damu Al’ummar Yankin da tuni wasu sun fara kaura daga gidajensu saboda tsira da rayukansu kasancewar lamarin na janyo raunata mutane maza da mata..

Wakilin karamar Hukumar Rimin gado da Tofa Hon Muhammad Bello Butu-Butu da wakilin Ungoggo a majalisar Hon Aminu Saadu dana Dambatta da na Garko da Kuma na Takai cikin wadanda suka goyi bayan kudirin..

Shugaban Majalisar dokokin ta Kano Rt Hon Jibril Samaila Falgore ya bayyana amincewar Majalisar..

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1189 days 15 hours 25 minutes 5 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1171 days 17 hours 6 minutes 30 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com